• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Thursday, May 14, 2026
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Minista ya jaddada muhimmiyar rawar kafafen yaɗa labarai a cikin al’umma

by WAKILIN MU
August 30, 2024
in Nijeriya
0
Minista ya jaddada muhimmiyar rawar kafafen yaɗa labarai a cikin al’umma

Alhaji Mohammed Idris

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

MINISTAN Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya sake jaddada muhimmiyar rawar da kafafen yaɗa labarai ke takawa wajen jagorantar al’umma, da inganta fahimtar juna, da kuma bayar da gudunmawa ga gagarumin cigaba.

Idris ya bayyana hakan ne a yayin ƙaddamar da wani shirin talabijin mai taken “Traverse China With Me,” wanda na haɗin gwiwa ne tsakanin Hukumar Talabijin ta Nijeriya (NTA) da kuma China Media Group (CMG) a ranar Alhamis a Cibiyar Al’adun Ƙasar Sin da ke Abuja.

A wajen taron, Idris ya bayyana cewa shirin zai ƙarfafa alaƙar da ke tsakanin gidajen talabijin na Nijeriya da kafofin watsa labarai na ƙasar Sin, wato Chaina.

Ya ƙara da cewa wannan shiri wani ɓangare ne na ƙoƙarin inganta alaƙa tsakanin al’ummar Nijeriya da Sin ta hanyar musayar al’adu da harshe, ta hanyar amfani da hanyoyin sadarwa na zamani da ake da su a ƙasashen biyu.

Ministan ya yaba wa hukumomin CMG da NTA bisa jajircewar su wajen samar da ingantattun labarai da shirye-shirye masu ma’ana waɗanda ke taimaka wa cigaban ƙasashen biyu.

Ya ce haɗin gwiwar zai yi tasiri mai kyau ga harkokin zamantakewa, cigaban tattalin arziki, da cigaban al’adu.

Idris ya kuma jaddada muhimmancin daidaita rahotanni, musamman wajen bayyana cigaban da aka samu, da kuma samar da shirye-shirye da za su haifar da kyakkyawar fatar samun cigaba a nan gaba.

Ya ce Nijeriya da ke da ɗimbin matasa tana fuskantar ƙalubale da dama da suka haɗa da yaɗa labaran ƙarya da ji-ta-ji-ta waɗanda ke haifar da koma-baya da rashin yarda tsakanin gwamnati da ‘yan ƙasar.

Ya buƙaci kafafen yaɗa labarai na Chaina da su haɗa kai da Nijeriya da sauran takwarorin su na ƙasa da ƙasa don daƙile wannan mummunar ɗabi’a da tabbatar da inganci da aminci a cikin harkar yaɗa labarai.

Bugu da ƙari, ministan ya yi kira ga CMG da ya faɗaɗa kafafen yaɗa labaran sa a Nijeriya ta hanyar haɗawa da wasu harsuna, kamar Hausa, Ibo, Yarbanci, da Pijin.

Ya ce hakan ba kawai zai inganta sadarwa ba, har ma zai samar da guraben aikin yi da horar da ‘yan Nijeriya.

Ita ma Daraktar Sashen Hausa na CMG, Kande Gao, ta yi jawabi a wajen taron, inda ta bayyana alaƙar da ke tsakanin Sin da Nijeriya, tare da yin kira da a ƙara yin hadin gwiwa.

Ta bayyana cewa kamfanin CMG ya himmatu wajen samar da fahimtar juna a tsakanin ƙasashen biyu, kamar yadda ake nunawa a cikin shirye-shirye irin su “Traverse China With Me,” wanda ya samu karɓuwa musamman a yankunan da ake magana da harshen Hausa.

Taron ya samu halartar wakilai daga NTA, gidan Rediyon Nijeriya, Muryar Nijeriya, da Hukumar Kula da Kafofin Yaɗa Labarai a Nijeriya.

Loading

Tags: ChinaCMGkafafen yaɗa labaraiKande GaoMohammed IdrisNTA
Previous Post

Zurfafa hulɗa da BBC zai taimaka wajen samun ƙara wayewar al’ummar mu, inji Minista

Next Post

Barka Da Zagayowar Ranar Haihuwar Ka Miji Na

Related Posts

Yadda CBN ke tallabe da tattalin arzikin Nijeriya, yayin sa farashin ɗanyen mai ke faɗuwar-‘yan-bori a kasuwa
Nijeriya

Yadda CBN ke tallabe da tattalin arzikin Nijeriya, yayin sa farashin ɗanyen mai ke faɗuwar-‘yan-bori a kasuwa

November 7, 2025
Shirin ƙarfafa jari: CBN ya shawarci bankuna marasa ƙarfi su haɗe ko su rage wa lasisin su geji
Nijeriya

Shirin ƙarfafa jari: CBN ya shawarci bankuna marasa ƙarfi su haɗe ko su rage wa lasisin su geji

November 2, 2025
Bankin CBN ya yunƙuro: Naira ta hana dala numfashi mai ƙarfi a ƙarshen Oktoba
Nijeriya

Bankin CBN ya yunƙuro: Naira ta hana dala numfashi mai ƙarfi a ƙarshen Oktoba

November 2, 2025
Bankin CBN ya ƙaryata ƙazafin sayar wa manyan dillalan mai dala biliyan 1.259 domin su shigo da fetur daga waje
Nijeriya

Bankin CBN ya ƙaryata ƙazafin sayar wa manyan dillalan mai dala biliyan 1.259 domin su shigo da fetur daga waje

October 29, 2025
Tinubu ya yi adalci ga dukkan yankunan Nijeriya – Ministan Yaɗa Labarai
Nijeriya

Tinubu ya yi adalci ga dukkan yankunan Nijeriya – Ministan Yaɗa Labarai

August 31, 2025
Nijeriya

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar da Sababbin Cibiyoyin Maganin Ciwon Daji

July 24, 2025
Next Post
Barka Da Zagayowar Ranar Haihuwar Ka Miji Na

Barka Da Zagayowar Ranar Haihuwar Ka Miji Na

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!