• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Wednesday, August 26, 2026
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Ministar Jinƙai ta jajanta kan mutuwar sojojin sama 7

by DAGA WAKILIN MU
February 21, 2021
in Nijeriya
0
Ministar Jinƙai ta jajanta kan mutuwar sojojin sama 7
0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

MINISTAR Harkokin Jinƙai, Agaji da Inganta Rayuwa, Hajiya Sadiya Umar Farouq, ta bayyana alhinin ta kan faɗowar jirgin saman Rundunar Mayaƙan Sama ta Nijeriya (NAF) ƙirar Beechcraft KingAir B350i Aircraft a ranar Lahadi a Abuja.


Rahotanni sun ce jirgin ya samu matsalar inji bayan ya tashi sannan ya faɗo ƙasa.


Hajiya Sadiya ta bayyana baƙin ciki kan haɗarin jirgin da kuma asarar rayukan waɗanda ke cikin jirgin da aka yi.


Ta ce, “Ina cikin tsananin alhini da baƙin cikin wannan abu maras daɗi da ya faru.

Ina miƙa gaisuwa ta ga Rundunar Mayaƙan Sama da iyalan waɗanda su ka ran su a faɗowar jirgin.


“Rundunar Mayaƙan Sama ta na bada matuƙar tallafi ga ayyukan mu na kai kayan agaji tun daga farkon kafa wannan Ma’aikata. 

“Sun taimaka wajen ɗaukar kayan agaji ga mutanen da wani abu ya faru gare su musamman a lokacin zaman tilas don rage yaɗuwar cutar korona a cikin shekarar 2020 da kuma zuwa ga waɗanda annobar ambaliya da harin ‘yan bindiga da rikice-rikicen jama’a da sauran bala’o’i su ka shafa. 


“Mu na godiya kan ayyukan ma’aikatan jiragen su, musamman matuƙan jiragen waɗanda su ka shafe ɗaruruwan awoyi su na tuƙa mu zuwa da dawowa ga yankunan da bala’o’i da sauran al’amuran jinƙai su ka shafa.


“Mu na addu’ar Allah ya bada haƙuri ga iyalan su da su ka bari a baya kuma ya ba su jimirin jure wannan rashi na masoyan su da su ka yi.”


Fasinjoji bakwai ne a cikin jirgin, ciki har da matuƙa biyu.


Hukumar Mayaƙan Sama ta bayyana cewa jirgin ya faɗo ne ranar Lahadi, 21 ga Fabrairu, 2021 a lokacin da ya yi ƙoƙarin dawowa Babban Filin Jirgin Sama na Nnamdi Azikiwe da ke Abuja jim kaɗan bayan ya samu matsalar inji a kan hanyar sa ta zuwa Minna. 

Hukumar ta ce jirgin ya tashi ne domin ya je ya yi shawagi a saman Jihar Neja da kewaye da nufin ko ma’aikatan za su ga wasu ɗalibai da malaman makaranta da aka sace daga Kwalejin Kimiyya ta Gwamnati da ke Kagara, Jihar Neja.


Mutum bakwai da su ka rasu a haɗarin su ne:


a. Flight Lieutenant Haruna Gadzama (direban jirgin)


b. Flight Lieutenant Henry Piyo (mataimakin direba)


c. Flying Officer Micheal Okpara (Airborne Tactical Observation System (ATOS) Specialist)


d. Warrant Officer Bassey Etim (ATOS Specialist)


e. Flight Sergeant Olasunkanmi Olawunmi (ATOS Specialist)


f. Sergeant Ugochukwu Oluka (ATOS Specialist)


g. Aircraftman Adewale Johnson (Onboard Technician).

Previous Post

Kama Mu’azzam: Afakallah ya yi wa su Falalu Ɗorayi da Baban Chinedu raddi

Next Post

Hukuma ta ƙwace finafinan batsa a Sakkwato

Related Posts

Yadda CBN ke tallabe da tattalin arzikin Nijeriya, yayin sa farashin ɗanyen mai ke faɗuwar-‘yan-bori a kasuwa
Nijeriya

Yadda CBN ke tallabe da tattalin arzikin Nijeriya, yayin sa farashin ɗanyen mai ke faɗuwar-‘yan-bori a kasuwa

November 7, 2025
Shirin ƙarfafa jari: CBN ya shawarci bankuna marasa ƙarfi su haɗe ko su rage wa lasisin su geji
Nijeriya

Shirin ƙarfafa jari: CBN ya shawarci bankuna marasa ƙarfi su haɗe ko su rage wa lasisin su geji

November 2, 2025
Bankin CBN ya yunƙuro: Naira ta hana dala numfashi mai ƙarfi a ƙarshen Oktoba
Nijeriya

Bankin CBN ya yunƙuro: Naira ta hana dala numfashi mai ƙarfi a ƙarshen Oktoba

November 2, 2025
Bankin CBN ya ƙaryata ƙazafin sayar wa manyan dillalan mai dala biliyan 1.259 domin su shigo da fetur daga waje
Nijeriya

Bankin CBN ya ƙaryata ƙazafin sayar wa manyan dillalan mai dala biliyan 1.259 domin su shigo da fetur daga waje

October 29, 2025
Tinubu ya yi adalci ga dukkan yankunan Nijeriya – Ministan Yaɗa Labarai
Nijeriya

Tinubu ya yi adalci ga dukkan yankunan Nijeriya – Ministan Yaɗa Labarai

August 31, 2025
Nijeriya

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar da Sababbin Cibiyoyin Maganin Ciwon Daji

July 24, 2025
Next Post
Hukuma ta ƙwace finafinan batsa a Sakkwato

Hukuma ta ƙwace finafinan batsa a Sakkwato

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!