• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Friday, June 6, 2025
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

MOPPAN ta taya Afakallahu murnar naɗin da Shugaba Tinubu ya yi masa

by ABBA MUHAMMAD
May 19, 2024
in Labarai
0
MOPPAN ta taya Afakallahu murnar naɗin da Shugaba Tinubu ya yi masa

Alhaji Isma'ila Muhammad Na'abba (Afakallahu)

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

ƘUNGIYAR Masu Shirya Finafinai ta Nijeriya (Motion Picture Practitioners Association of Nigeria, MOPPAN), ƙarƙashin jagorancin Alhaji Habibu Mohammed Barde, ta miƙa saƙon taya murna ga tsohon Babban Sakataren Hukumar Tace Finafinai da Ɗab’i ta Jihar Kano, Alhaji Isma’ila Muhammad Na’abba (Afakallahu), kan naɗin da Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya yi masa a matsayin memba na Hukumar Gudanarwa ta Jami’ar Tarayya da ke Dutse, Jihar Jigawa.

Shugaban ƙungiyar, Alhaji Habibu Mohammed Barde, ya yaba wa Afakallahu a matsayin ɗaya daga cikin jiga-jigan masana’antar finafinai ta Hausa, wato Kannywood.

Ya ce ƙwazon sa da gudunmawar da ya bayar sun tsara yanayin masana’antar sosai, wanda hakan ya sa wannan naɗin ya zama abin da ya dace daga kyakkyawar hidima da jajircewar sa.

Shugaban ya tuna da zaman Afakallahu a matsayin Babban Sakataren Hukumar Tace Finafinai ta Jihar Kano a matsayin abin koyi tare da himma sosai wajen tabbatar da ƙa’idoji da ɗa’a na Kannywood.

Ya ƙara da cewa, “Sabuwar rawar da zai taka a Hukumar Gudanarwar Jami’ar Tarayya ta Jigawa wata shaida ce ta ci gaba da sadaukar da kai ga aikin gwamnati da cigaban ilimi da al’adu a Nijeriya.”

An bayar da wannan yabo ne cikin alfahari da mutunta irin goyon bayan da Afakallahu ke bayarwa da kuma gudunmawa mai kima ga masana’antar fim.

MOPPAN, a cewar sanarwa ga manema labarai wadda Sakataren Yaɗa Labarai na MOPPAN na ƙasa, Malam Al-Amin Ciroma, ya sanya wa hannu, ta ce ta na da yaƙinin cewa ƙwarewa da gogewar Afakallahu za su amfanar da Jami’ar Tarayya ta Dutse sosai tare da ƙara inganta manufar ta ta fasaha da ilimi.

Tsohon babban sakataren Hukumar Tace Finafinai ta Jihar Kano, Afakallahu ya samu muƙami a Jami’ar Tarayya da ke Dutse, Jihar Jigawa

Shi dai Afakallahu, ya samu wannan naɗi ne a ranar Juma’a, 17 ga Mayu, lokacin da Gwamnatin Tarayya ta bayyana naɗin aƙalla mutum 554 a matsayin membobin ‘yan hukumomin gudanarwa na jami’o’i da makarantun kimiyya da fasaha 111 da ke faɗin ƙasar nan.

Bayan sanar da amincewar naɗin nasu ne, Afakallahu ya yi wa shugaban ƙasa godiya a Instagram inda ya fara da yi wa Allah godiya da cewa, “Alhamdu lillah, Alhamdu lillah. Allah ya ƙara yi.”

Sannan sai ya ce, “Ni Isma’ila Muhammad Na’abba Afakallah da dukkan iyali na, mu na miƙa godiyar mu ga shugaban ƙasa kuma kwamandan rundunar sojin ƙasa, Bola Ahmed Tinubu (Jagaban), domin naɗa ni a matsayin memba na Hukumar Gudanarwa ta Jami’ar Gwamnatin Tarayya da ke Dutse, Jihar Jigawa. Ina ƙara yi wa Allah godiya.”

A ranar Alhamis, 30 ga Mayu da Juma’a, 31 ga Mayu, 2024 ne za a ƙaddamar da Hukumomin Gudanarwar a Hukumar Jami’o’i ta Ƙasa (NUC) da ke Abuja.

A halin yanzu dai Afakallahu shi ne mutum na uku da ya samu muƙami a wannan gwamnati kuma ɗan fim na farko da aka naɗa memba na Hukumar Gudanarwar wata jami’a a ƙasar nan.

Loading

Tags: Habibu Barde MuhammadIsma'ila Na'abba AfakallahuJami'ar Tarayya Dutse
Previous Post

Ministan Yaɗa Labarai ya yi alƙawarin tallafa wa gidan Rediyon EFCC

Next Post

MOPPAN ta kafa kwamitocin ladabtarwa da tara kuɗaɗe don inganta nagartar Kannywood

Related Posts

An naɗa Shehu Hassan Kano shugaban riƙo na MOPPAN
Labarai

An naɗa Shehu Hassan Kano shugaban riƙo na MOPPAN

June 3, 2025
MOPPAN ta ba gwamnan Kebbi lambar yabo a madadin ‘yan fim
Labarai

MOPPAN ta ba gwamnan Kebbi lambar yabo a madadin ‘yan fim

June 2, 2025
Ƙungiya ta ja kunnen gwamnatin Kano kan dakatar da finafinan Kannywood 22
Labarai

Ƙungiya ta ja kunnen gwamnatin Kano kan dakatar da finafinan Kannywood 22

May 20, 2025
Hukuma ta rufe gidajen gala a Kano har sai bayan Ramadan
Labarai

Gwamnatin Kano ta dakatar da haska finafinan Kannywood 22 a intanet da talbijin 

May 19, 2025
Labarai

Gwamnan Kano ya ɗauki nauyin ‘yan Kannywood 5 zuwa Hajjin bana

April 17, 2025
Sabuwa, matar Ɗanmaraya Jos, ta rasu
Labarai

Sabuwa, matar Ɗanmaraya Jos, ta rasu

March 28, 2025
Next Post
MOPPAN ta kafa kwamitocin ladabtarwa da tara kuɗaɗe don inganta nagartar Kannywood

MOPPAN ta kafa kwamitocin ladabtarwa da tara kuɗaɗe don inganta nagartar Kannywood

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!