• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Wednesday, July 30, 2025
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

MOPPAN ta taya Afakallahu murnar naɗin da Shugaba Tinubu ya yi masa

by ABBA MUHAMMAD
May 19, 2024
in Labarai
0
MOPPAN ta taya Afakallahu murnar naɗin da Shugaba Tinubu ya yi masa

Alhaji Isma'ila Muhammad Na'abba (Afakallahu)

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

ƘUNGIYAR Masu Shirya Finafinai ta Nijeriya (Motion Picture Practitioners Association of Nigeria, MOPPAN), ƙarƙashin jagorancin Alhaji Habibu Mohammed Barde, ta miƙa saƙon taya murna ga tsohon Babban Sakataren Hukumar Tace Finafinai da Ɗab’i ta Jihar Kano, Alhaji Isma’ila Muhammad Na’abba (Afakallahu), kan naɗin da Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya yi masa a matsayin memba na Hukumar Gudanarwa ta Jami’ar Tarayya da ke Dutse, Jihar Jigawa.

Shugaban ƙungiyar, Alhaji Habibu Mohammed Barde, ya yaba wa Afakallahu a matsayin ɗaya daga cikin jiga-jigan masana’antar finafinai ta Hausa, wato Kannywood.

Ya ce ƙwazon sa da gudunmawar da ya bayar sun tsara yanayin masana’antar sosai, wanda hakan ya sa wannan naɗin ya zama abin da ya dace daga kyakkyawar hidima da jajircewar sa.

Shugaban ya tuna da zaman Afakallahu a matsayin Babban Sakataren Hukumar Tace Finafinai ta Jihar Kano a matsayin abin koyi tare da himma sosai wajen tabbatar da ƙa’idoji da ɗa’a na Kannywood.

Ya ƙara da cewa, “Sabuwar rawar da zai taka a Hukumar Gudanarwar Jami’ar Tarayya ta Jigawa wata shaida ce ta ci gaba da sadaukar da kai ga aikin gwamnati da cigaban ilimi da al’adu a Nijeriya.”

An bayar da wannan yabo ne cikin alfahari da mutunta irin goyon bayan da Afakallahu ke bayarwa da kuma gudunmawa mai kima ga masana’antar fim.

MOPPAN, a cewar sanarwa ga manema labarai wadda Sakataren Yaɗa Labarai na MOPPAN na ƙasa, Malam Al-Amin Ciroma, ya sanya wa hannu, ta ce ta na da yaƙinin cewa ƙwarewa da gogewar Afakallahu za su amfanar da Jami’ar Tarayya ta Dutse sosai tare da ƙara inganta manufar ta ta fasaha da ilimi.

Tsohon babban sakataren Hukumar Tace Finafinai ta Jihar Kano, Afakallahu ya samu muƙami a Jami’ar Tarayya da ke Dutse, Jihar Jigawa

Shi dai Afakallahu, ya samu wannan naɗi ne a ranar Juma’a, 17 ga Mayu, lokacin da Gwamnatin Tarayya ta bayyana naɗin aƙalla mutum 554 a matsayin membobin ‘yan hukumomin gudanarwa na jami’o’i da makarantun kimiyya da fasaha 111 da ke faɗin ƙasar nan.

Bayan sanar da amincewar naɗin nasu ne, Afakallahu ya yi wa shugaban ƙasa godiya a Instagram inda ya fara da yi wa Allah godiya da cewa, “Alhamdu lillah, Alhamdu lillah. Allah ya ƙara yi.”

Sannan sai ya ce, “Ni Isma’ila Muhammad Na’abba Afakallah da dukkan iyali na, mu na miƙa godiyar mu ga shugaban ƙasa kuma kwamandan rundunar sojin ƙasa, Bola Ahmed Tinubu (Jagaban), domin naɗa ni a matsayin memba na Hukumar Gudanarwa ta Jami’ar Gwamnatin Tarayya da ke Dutse, Jihar Jigawa. Ina ƙara yi wa Allah godiya.”

A ranar Alhamis, 30 ga Mayu da Juma’a, 31 ga Mayu, 2024 ne za a ƙaddamar da Hukumomin Gudanarwar a Hukumar Jami’o’i ta Ƙasa (NUC) da ke Abuja.

A halin yanzu dai Afakallahu shi ne mutum na uku da ya samu muƙami a wannan gwamnati kuma ɗan fim na farko da aka naɗa memba na Hukumar Gudanarwar wata jami’a a ƙasar nan.

Loading

Tags: Habibu Barde MuhammadIsma'ila Na'abba AfakallahuJami'ar Tarayya Dutse
Previous Post

Ministan Yaɗa Labarai ya yi alƙawarin tallafa wa gidan Rediyon EFCC

Next Post

MOPPAN ta kafa kwamitocin ladabtarwa da tara kuɗaɗe don inganta nagartar Kannywood

Related Posts

Wani mai suna Bashir Abdullahi ya damfare ni miliyan bakwai da rabi, inji Halisa
Labarai

Wani mai suna Bashir Abdullahi ya damfare ni miliyan bakwai da rabi, inji Halisa

July 28, 2025
Gaskiyar magana kan ji-ta-ji-tar ‘mutuwar’ Aminu Ala
Labarai

Gaskiyar magana kan ji-ta-ji-tar ‘mutuwar’ Aminu Ala

July 28, 2025
Labarai

KADIFF 2025: Uganda ta fi yawan finafinai a bikin baje-kolin na Kaduna – Israel Kashim Audu

July 25, 2025
Labarai

Karya dokar liƙi: Kotu ta ɗaure G-Fresh da Hamisu Breaker tsawon wata biyar-biyar

July 24, 2025
‘Yan Kannywood sun kaɗu da rasuwar Abdoulfatah Omar
Labarai

‘Yan Kannywood sun kaɗu da rasuwar Abdoulfatah Omar

July 23, 2025
Allah ya yi wa mahaifiyar darakta Salisu Mu’azu rasuwa
Labarai

Allah ya yi wa mahaifiyar darakta Salisu Mu’azu rasuwa

July 17, 2025
Next Post
MOPPAN ta kafa kwamitocin ladabtarwa da tara kuɗaɗe don inganta nagartar Kannywood

MOPPAN ta kafa kwamitocin ladabtarwa da tara kuɗaɗe don inganta nagartar Kannywood

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!