TUN bayan buɗe sabon ofis da Ƙungiyar Jaruman Kannywood ta Jihar Kano ta yi daga bayan Kantin Jifatu da ke Titin Zariya zuwa Titin Adamu Ɗankura da kuma zaman da sauran shugabannin ta irin su Tijjani Asase da Ƙazaza su ke yi a tsohon ofin ɗin ake ta yaɗa maganganu a kan ƙungiyar, har ana cewa ta rabu gida biyu.
Da mujallar Fim ta nemi jin ta bakin shugaban ƙungiyar, Malam Alhasan Kwalle, sai ya shaida mana cewa,”Ƙungiyar Jarumai ba rabuwa ta yi ba, mu na nan a tare mu na aiki tare, kawai dai an samu sauyin ofishin ƙungiyar ne daga bayan Jifatu zuwa Titin Adamu Ɗankura.”
A kan dalilin ci gaba da ganin tsohon ofishin a buɗe kuma sauran shugabannin ƙungiyar su na a zaune a wajen su na gudanar da harkokin su, Alhassan, wanda ake wa laƙabi da Baƙin Wake, ya ce, “Wannan haka ne. Su Tijjani Asase su na tsohon ofin. Amma ba da sunan Ƙungiyar Jarumai su ke zama ba. Su na zama ne a matsayin kamfanin su da su ke gudanar da harkar fim ɗin ‘A Duniya’. Don haka duk wani abu da ya shafi aikin fim ɗin a ciki su ke yi, amma ba na Ƙungiyar Jarumai ba ne.”
Da mu ka tambaye shi dalilin tashin ofis daga wajen tunda ba rabuwa aka yi ba, sai ya ce, “To gaskiya wajen tun farko da mu ka zauna mu kaɗai ne a wajen, a yanzu sai ya zama an buɗe wajen shaƙatawa a wajen, sai ya zama samari da mata su na zuwa, kuma akwai waɗanda ba abin kirki ya ke kawo su wajen ba.
“Kuma ‘yan Hisbah su na yawan kawo hari wajen. To kuma daga sun zo, sai matan su riƙa zuwa su na shiga ofishin mu su na ɓuya, don haka sai ya zama ana tunanin ‘yan fim ne. Don akwai lokacin da har ciki ‘yan Hisbah su ka shiga su ka kamo wasu matan.
“To wannan ya sa mu ka ga ana nema a ɓata wa harkar fim suna. Don haka sai mu ka tashi daga wajen, domin zaman mu a wajen zai iya kowa ɓata sunan masana’antar fim, mu kuma ba don haka mu ke zama a wajen ba.
“Kuma tun da abin ya zo da haka mu ka ga ya dace mu bar wajen, mu koma wajen da za mu kiyaye martabar masana’antar, domin ba za mu so harkar da mu ka ɗauki shekaru mu na ƙoƙarin gyara ta ba kuma wani abu ya zo wanda zai mayar da hannun agogo baya ba, don haka ne mu ka tashi daga wajen.”
Alhasan Kwalle ya yi kira ga ‘yan fim da su riƙa kiyaye mutuncin su da na sana’ar su a duk inda su ka samu kan su.