• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Sunday, April 5, 2026
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Ranar Al’adu ta Duniya: Gwamnan Kano na so a yi riƙo da al’adun gargajiya

by MUKHTAR YAKUBU
August 10, 2025
in Al'adu
0
Gwamna Abba Kabir Yusuf yana Jawabi a wajen taron

Gwamna Abba Kabir Yusuf yana Jawabi a wajen taron

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

Gwamna Abba Kabir Yusuf na Jihar Kano ya jaddada muhimmancin raya al’adun gargajiya da kuma bunƙasa su domin amfanin matasa da ‘yan baya.

Ya ce gwamnati za ta ci gaba da tallafa wa shirye-shiryen da ke da nasaba da bunƙasa al’adu da kuma ilimantar da jama’a game da su.

Gwamnan ya bayyana haka ne a taron bikin Ranar Al’adun Gargajiya ta Duniya wanda ake yi duk ranar 3 ga Agusta na kowace shekara.

Ma’aikatar Raya Al’adun Gargajiya da Yawon Buɗe Ido ta Jihar Kano ce ta shirya taron, wanda aka gudanar a babban ɗakin taro na Fadar Gwamnatin Jihar Kano, wato Coronation Hall.

Gwamnan ya ce: “Al’adu su ne ginshikin kowacce al’umma. Idan muka rasa su, to kamar mun rasa tushe ne.

An gudanar da taron ne domin tunawa da muhimmancin al’adu da kuma ƙara wayar da kai game da rawar da suke takawa wajen tabbatar da zaman lafiya da cigaban al’umma.

A jawabin da ta gabatar kan manufar taron, Kwamishinar Raya Al’adun Gargajiya da Yawon Buɗe Ido ta Jihar Kano, Hajiya A’isha Lawan Saje Rano, ta bayyana al’adun gargajiya a matsayin wani tushe na cigaban al’umma wanda hakan ya sa aka ware duk ranar 3 ga Agusta domin yin bikin Ranar Al’adun Gargajiya ta Duniya.

Kwamishiniyar Ma'aikatar Raya Al'adun Gargajiya da Yawon Buɗe idanu, Hajiya Aisha Lawan Saje Rano, tana Jawabi a wajen taron
Kwamishinar Raya Al’adun Gargajiya da Yawon Buɗe ido, Hajiya Aisha Lawan Saje Rano, tana jawabi a wajen taron

Ta ce: “Don haka ne a wannan shekara muka bai wa ranar muhimmanci domin nuna wa mutane, musamman matasan mu, muhimmancin wannan rana. Manufar mu dai ita ce koyar da al’umma ci gaba da riƙo da al’adun gargajiya.”

A taron, Ma’aikatar Raya Al’adun Gargajiya da Yawon Buɗe Ido ta Jihar Kano ta shirya baje-kolin kayayyakin gargajiya da al’adun Hausawa wanda ya haɗa da wasannin gargajiya, raye-raye, kiɗan gargajiya da kuma nune-nunen sana’o’in hannu na mutanen Kano, lamarin da ya ƙara ƙayatar da mahalarta taron.

Taron ya samu halartar manyan baƙi daga sassa daban-daban na Jihar Kano da ma ƙasa baki ɗaya, ciki har da shugabannin al’umma, malamai, da masu ruwa da tsaki a harkar raya al’adu.

Loading

Previous Post

Jarumar Kannywood, Rahama Sadau ta yi aure

Next Post

Bayan auren Rahama Sadau, ido ya koma kan Gabon, Nafisat, Washa, Amal da wasu ‘yan matan na Kannywood 

Related Posts

Al'adu

Kare Sabbin Kalmomin Hausa “Saskiyā” (Synonym) da “Gīɗiyā” (Antonym) ta Hanyar ‘Yancin Binciken Ilimi

May 22, 2025
Sarkin Kano Muhammadu Sanusi II kadara ne mai daraja ga Jihar Kano
Al'adu

Sarkin Kano Muhammadu Sanusi II kadara ne mai daraja ga Jihar Kano

January 28, 2024
Minista Hannatu Musawa ta ƙudiri aniyar kafa Gidan Tarihi da Gidan Wasanni na Ƙasa a Abuja
Al'adu

Minista Hannatu Musawa ta ƙudiri aniyar kafa Gidan Tarihi da Gidan Wasanni na Ƙasa a Abuja

December 14, 2023
Khalifa Muhammadu Sanusi II
Al'adu

Sanusi: Magajin Sanusi da Kukuna

June 23, 2023
Shugabannin ƙasashen Afrika a wajen wani babban taron su a Habasha
Al'adu

Ƙungiyar Tarayyar Afrika ta zaɓi Swahili a matsayin harshen da za ta riƙa aiki da shi

February 10, 2022
Marigayi Alh. Mamman Raba-Gardama. Hoto daga: Abdulaziz Abdulaziz
Al'adu

Ta’aziyyar Muhammadu Ɗan Sanyinna (Raba-Gardama)

January 11, 2022
Next Post
Bayan auren Rahama Sadau, ido ya koma kan Gabon, Nafisat, Washa, Amal da wasu ‘yan matan na Kannywood 

Bayan auren Rahama Sadau, ido ya koma kan Gabon, Nafisat, Washa, Amal da wasu 'yan matan na Kannywood 

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!