• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Wednesday, July 23, 2025
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Sabon shirin ‘N-Knowledge’ zai horas da matasan Nijeriya 20,000 kan fasahar zamani – Minista Sadiya

by DAGA WAKILIN MU
November 8, 2021
in Nijeriya
0
Hajiya Sadiya Umar Farouq

Hajiya Sadiya Umar Farouq

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

MINISTAR Harkokin Jinƙai, Agaji da Inganta Rayuwa, Hajiya Sadiya Umar Farouq, ta bayyana cewa Gwamnatin Tarayya ta soma aiwatar da wani sabon shiri mai suna ‘N-Knowledge’ domin tallafa wa matasan Nijeriya su koyi aikin yi a ɓangaren fasahar zamani.

A wata sanarwa da aka raba wa manema labarai, Babban Sakataren ma’aikatar, Alhaji Bashir Nura Alƙali, ya bayyana cewa an fara shirin ne a dukkan sassa shida na ƙasar nan tare da Yankin Babban Birnin Tarayya, Abuja, kuma wani ɓangare ne na shirin nan na ‘N-Power’.

Alƙali ya ce, “‘N-Knowledge’ wani ɓangare ne na shirin ‘N-Power’ wanda zai maida hankali ga bai wa matasan Nijeriya horaswar da ta kamata tare da satifiket domin su zama ƙwararrun ma’aikata, masu ƙirƙira kuma ‘yan kasuwa da za su iya yin aiki a cikin gida da ƙasar waje.

“Shirin na ‘N-Power (N-Knowledge)’ zai horas da matasa 20,000 daidai da muradin duniya a matsayin waɗanda za su iya yin aiki a ƙasashen waje a ɓangaren fasahar harkokin komfuta da intanet.”
Babban Sakataren ya ce an tsara ɓangaren horaswa na shirin ne don bunƙasa ƙwarewar matasan wajen ƙirƙirar manhaja da horaswa kan haɗawa da gyara kayan aikin komfuta wanda zai sanya Nijeriya ta shiga sahun ƙasashen da ke tura ma’aikata zuwa wasu ƙasashen domin su yi aikin haɗa manhaja.
A cewar sa, “Shirin zai samar da ƙwarewa da iyawa a fagen tsara manhajojin wayar hannu da gina gidajen yana tare da inganta basira don a haɓaka masana’antar fasahar yaɗa labarai da ilimin intanet a Nijeriya.
“Shirin ya ƙunshi aje matasa a wani keɓaɓɓen wuri ana horas da su har tsawon wata uku sannan a ba su aikin wucin gadi na wata shida a dukkan sassa shida na ƙasar nan. 

“Jimillar mutum 20,000 za su ci moriyar shirin.”
Ya ƙara da cewa a ƙarshen shirin, matasan da aka gamsu da cancantar su daga horaswar da aka yi masu za a ba su satifiket da takardun shaida. 

Ya ce, “A lokacin wannan tirenin ɗin za a yi masu karatu daban-daban wanda ba shakka zai ƙara masu sanin makamar aiki har su kasance sun shirya wa shiga duk wata gogayya a duniya wajen aiki. 

“Wannan ya na da muhimmanci domin kuwa waɗanda aka horas ɗin za a koya masu darussan da za su amfane su a iya tsawon rayuwar su tare da sauya masu tunani, da ɗabi’u nagari na gudanar da aiki a yayin da kuma ake karantar da su ƙa’idojin yin mu’amala da juna.”

Loading

Tags: agajiBashir Nura AlkaliDisaster Management and Social Developmentfasahar zamanihoraswamatasaMinistry of Humanitarian AffairsN-KnowledgeN-PowerSadiya Umar Farouqsatifiket
Previous Post

Mansurah na so gwamnati ta sa a riƙa nuna finafinan Hausa a dukkan sinimun Nijeriya

Next Post

Zaɓen Anambra bai kammalu ba, inji INEC

Related Posts

Sanatan Kaduna: Yerima Shettima za mu yi, inji ‘yan fim
Nijeriya

Sanatan Kaduna: Yerima Shettima za mu yi, inji ‘yan fim

July 15, 2025
Nijeriya

Tinubu yana goyon bayan Ƙananan Hukumomi su ci gashin kan su – Minista

July 11, 2025
Nijeriya

Shirin Sabunta Fata na Tinubu yana samar da damarmakin cigaba — Minista

July 10, 2025
Sauye-sauyen Tinubu suna taimaka wa farfaɗowar tattalin arzikin Nijeriya — Minista
Nijeriya

Sauye-sauyen Tinubu suna taimaka wa farfaɗowar tattalin arzikin Nijeriya — Minista

July 10, 2025
Ministoci za su fara gabatar da rahoton ayyuka a taron manema labarai
Nijeriya

Tinubu ba zai yarda hayaniyar siyasar 2027 ta ɗauke masa hankali ba – Minista

July 8, 2025
Ƙungiyoyi sun buƙaci bayanai daga ‘yan sanda kan harin da aka kai fadar Sarkin Kano
Nijeriya

Ƙungiyoyi sun buƙaci bayanai daga ‘yan sanda kan harin da aka kai fadar Sarkin Kano

July 8, 2025
Next Post
Farfesa Florence Obi ta na bada sanarwa ga manema labarai kan zaɓen Anambra ɗazu a garin Awka

Zaɓen Anambra bai kammalu ba, inji INEC

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!