• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Saturday, June 7, 2025
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Sabon shirin ‘N-Knowledge’ zai horas da matasan Nijeriya 20,000 kan fasahar zamani – Minista Sadiya

by DAGA WAKILIN MU
November 8, 2021
in Nijeriya
0
Hajiya Sadiya Umar Farouq

Hajiya Sadiya Umar Farouq

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

MINISTAR Harkokin Jinƙai, Agaji da Inganta Rayuwa, Hajiya Sadiya Umar Farouq, ta bayyana cewa Gwamnatin Tarayya ta soma aiwatar da wani sabon shiri mai suna ‘N-Knowledge’ domin tallafa wa matasan Nijeriya su koyi aikin yi a ɓangaren fasahar zamani.

A wata sanarwa da aka raba wa manema labarai, Babban Sakataren ma’aikatar, Alhaji Bashir Nura Alƙali, ya bayyana cewa an fara shirin ne a dukkan sassa shida na ƙasar nan tare da Yankin Babban Birnin Tarayya, Abuja, kuma wani ɓangare ne na shirin nan na ‘N-Power’.

Alƙali ya ce, “‘N-Knowledge’ wani ɓangare ne na shirin ‘N-Power’ wanda zai maida hankali ga bai wa matasan Nijeriya horaswar da ta kamata tare da satifiket domin su zama ƙwararrun ma’aikata, masu ƙirƙira kuma ‘yan kasuwa da za su iya yin aiki a cikin gida da ƙasar waje.

“Shirin na ‘N-Power (N-Knowledge)’ zai horas da matasa 20,000 daidai da muradin duniya a matsayin waɗanda za su iya yin aiki a ƙasashen waje a ɓangaren fasahar harkokin komfuta da intanet.”
Babban Sakataren ya ce an tsara ɓangaren horaswa na shirin ne don bunƙasa ƙwarewar matasan wajen ƙirƙirar manhaja da horaswa kan haɗawa da gyara kayan aikin komfuta wanda zai sanya Nijeriya ta shiga sahun ƙasashen da ke tura ma’aikata zuwa wasu ƙasashen domin su yi aikin haɗa manhaja.
A cewar sa, “Shirin zai samar da ƙwarewa da iyawa a fagen tsara manhajojin wayar hannu da gina gidajen yana tare da inganta basira don a haɓaka masana’antar fasahar yaɗa labarai da ilimin intanet a Nijeriya.
“Shirin ya ƙunshi aje matasa a wani keɓaɓɓen wuri ana horas da su har tsawon wata uku sannan a ba su aikin wucin gadi na wata shida a dukkan sassa shida na ƙasar nan. 

“Jimillar mutum 20,000 za su ci moriyar shirin.”
Ya ƙara da cewa a ƙarshen shirin, matasan da aka gamsu da cancantar su daga horaswar da aka yi masu za a ba su satifiket da takardun shaida. 

Ya ce, “A lokacin wannan tirenin ɗin za a yi masu karatu daban-daban wanda ba shakka zai ƙara masu sanin makamar aiki har su kasance sun shirya wa shiga duk wata gogayya a duniya wajen aiki. 

“Wannan ya na da muhimmanci domin kuwa waɗanda aka horas ɗin za a koya masu darussan da za su amfane su a iya tsawon rayuwar su tare da sauya masu tunani, da ɗabi’u nagari na gudanar da aiki a yayin da kuma ake karantar da su ƙa’idojin yin mu’amala da juna.”

Loading

Tags: agajiBashir Nura AlkaliDisaster Management and Social Developmentfasahar zamanihoraswamatasaMinistry of Humanitarian AffairsN-KnowledgeN-PowerSadiya Umar Farouqsatifiket
Previous Post

Mansurah na so gwamnati ta sa a riƙa nuna finafinan Hausa a dukkan sinimun Nijeriya

Next Post

Zaɓen Anambra bai kammalu ba, inji INEC

Related Posts

Gwamnatin Tarayya za ta tallafa wa yekuwar rigakafin cutar ƙyandar Jamus
Nijeriya

Gwamnatin Tarayya za ta tallafa wa yekuwar rigakafin cutar ƙyandar Jamus

June 4, 2025
Tinubu ya tura wakilai zuwa Neja kan ambaliyar Mokwa da ta halaka sama da mutum 150
Nijeriya

Tinubu ya tura wakilai zuwa Neja kan ambaliyar Mokwa da ta halaka sama da mutum 150

May 31, 2025
Gwamnatin Nijeriya ta goyi bayan amfani da Ƙirƙirarrar Basira cikin ɗa’a a aikin jarida – Idris
Nijeriya

Gwamnatin Tarayya ta yi ta’aziyyar mutanen da suka rasu a ambaliyar garin Mokwa

May 30, 2025
Babu wasu masu juya Tinubu ta bayan fage – Idris
Nijeriya

Babu wasu masu juya Tinubu ta bayan fage – Idris

May 25, 2025
Shirye-shiryen Shugaba Tinubu Suna Buɗe Hanyar Farfaɗowar Tattalin Arzikin Nijeriya – Idris
Nijeriya

Shirye-shiryen Shugaba Tinubu Suna Buɗe Hanyar Farfaɗowar Tattalin Arzikin Nijeriya – Idris

May 20, 2025
Idris ya ƙaryata ji-ta-ji-tar an mayar da taron bayanin ministoci zuwa London
Nijeriya

Idris ya ƙaryata ji-ta-ji-tar an mayar da taron bayanin ministoci zuwa London

May 16, 2025
Next Post
Farfesa Florence Obi ta na bada sanarwa ga manema labarai kan zaɓen Anambra ɗazu a garin Awka

Zaɓen Anambra bai kammalu ba, inji INEC

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!