ALLAHU Akbar! Allah ya yi wa matar fitaccen mawaƙi Alhaji Adamu Ɗanmaraya Jos, wato Hajiya Sabuwa Ɗanmaraya, rasuwa.
Ta rasu a garin Jos, Jihar Filato, a yau Juma’a bayan rashin lafiya.
An yi jana’izar ta yau da safe.
Hajiya Sabuwa da Ɗanmaraya dai Allah bai ba su haihuwa ba, to amma sun riƙe ‘ya’ya riƙo na amana kamar su suka haife su.
Shi Ɗanmaraya Jos ya rasu ne a ranar 20 ga Yuni, 2015, a Jos.
Allah ya jiƙan Hajiya Sabuwa da mijin ta Ɗanmaraya, amin.
