ALLAH cikin ikon sa ya ƙara azurta fitaccen mawaƙi Sagir Mustapha Ɗanyaro (Baban Kausar) da santala-santalan ‘ya’ya mata ‘yan biyu a safiyar jiya Talata, 3 ga Agusta, 2021.
Baban Kausar da kan sa ya bada sanarwa wannan ƙaruwar WhatsApp inda ya ce, “Salamu alaikum ‘yan’uwa ma’abota zumunci. Ina farin cikin sanar da ku cewa an yi wa mata ta CS, wato tiyata, da safen nan a asibitin Kadpoly, kuma an samu nasarar fiddo ‘ya’ya biyu tagwaye, duka mata.
“Mu na barar adu’ar ku da fatan samun lafiyar mahaifiyar da fatan Allah ya ba mu ikon kula da su bisa koyarwar addinin Musulunci, ameen.”
Mujallar Fim ta taɓa ba ku labarin cewa a ranar 9 ga Fabrairu, 2019 aka ɗaura auren Sagir Baban Kausar da matar sa Fatima Muhammad.

Fatima ta haifi ‘yar ta ta farko a ranar Laraba, 20 ga Nuwamba, 2019 da misalin ƙarfe 2:00 na dare, a asibitin Kwalejin Kimiyya Da Fasaha ta Kaduna (Kaduna Polytechnic) da ke Tudun Wada, Kaduna.
A dai wannan asibitin ne ta haifi ‘yan biyun ta jiya.
A yanzu Sagir na da ‘ya’ya huɗu kenan duk mata. Ta farko Kausar, ‘yar matar sa ta farko da ta rasu, sai kuma Fatima, wadda su ke kira da Zahra, sababbin tagwayen da su ka samu a jiya.
Mu na fatan Allah ya raya su cikin koyarwar addinin Musulunci, ita kuma mahaifiyar su Allah ya ba ta lafiya.