AN haifi marigayi Sheikh Alhaji Ahmad Tijjani Tukur Yola a watan Janairu, 1935, a unguwar Satatima cikin birnin Kano. Ya fara karatun allo tun ya na yaro har ya sauke Alƴur’ani a cikin 1948, wato ya na ɗan shekara 13.
Daga nan sai ya fara karatun ilimin addini da na harshen Larabci a wajen mahaifin sa, Malam Tukur Yola.
Bai bar karatu gare shi ba har sai da mahaifin nasa ya koma ƙauye da aiki. Daga nan sai ya juya wajen malaman gari don cigaba da neman ilimin sa.
Ya yi karatu wurin malamai da dama kafin ya shiga makarantar Shari’a ta Shahuci a shekarar 1955.
Bayan ya gama wannan makarantar sai ya tafi makarantar firamare ta Gwarzo, inda ya shekara biyu ya na koyo.
A cikin 1960 ya fara aikin koyarwa, har zuwa 1966, lokacin da ya shiga makarantar koyon harshen Larabci don ƙaro ilimi. Bayan ya gama a cikin 1969, ya sami takardar shaidar ilimin addinin Musulunci mai zurfi, sai ya koma kan aikin sa na koyarwa.
Bai daɗe ba kuma ya koma Kwalejin Abdullahi Bayero ta Jami’ar Ahmadu Bello don neman digiri, wanda ya kammala a shekarar 1976. Ya cigaba da aikin sa na koyarwa.
Sheikh Tijjani Tukur Yola babban marubuci ne adibi, malami masanin addinin Musulunci, wanda ya ƙare rayuwar sa a ilmantar da al’umma ta fannoni da dama. Haka za, ya yi wa harshen Hausa gagarumin aikin da duniyar nazarin harshen Hausa ba za ta taɓa mantawa da shi ba.
Daga cikin rubuce-rubucen sa na Hausa akwai waƙoƙi masu yawa da su ke ƙunshe da ɗimbin hikimomi da fasaha, gami da zalaƙar sarrafa harshe, da saƙwanni masu ma’ana cikin salo mai ban sha’awa.
Ya fara rubuta waƙa a cikin 1950 bisa sha’awar sa ta rubuce-rubucen waƙoƙi. Ya rubuta waƙoƙi da dama a kan addini da wa’azi, da siyasa da zamantakewar al’uma da sauran su. Kaɗan daga cikin waƙoƙin sa sun haɗa da:
1. “Ɗan’adam Kayan Allah”
2. “Duniya Ba Ki Da Gaskiya”
3. “Kanari”
4. “Cida”
5. “Hawainiya”
6. “Garkuwa”
7. “Allantaka”
8. “Mudi Da Siyasa”
9. “Uwa Ta Maganin Wahala Ta”
10. “Kar Ka Shigo”
11. “Mawaƙin Gaskiya”
12. “Ilimi Arziki Ne”
13. “Hausa Gwana”
14. “‘Yar Sarki”
15. “Burin Zuciya”
16. “Burtalin Dila”
17. “Hanyar Waliyyai”
Marigayi Sheikh Ahmad Tijjani Tukur Yola ya rasu a garin Kano a ranar Talata, 28 ga Afrilu, 2020 wanda yai daidai da ranar 5 ga Ramadan, 1441.
Allah ya jiƙan sa, ya gafarta masa ya sa can ta fi nan, amin.
Aysha Bilkisu Umar
28/4/20