• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Monday, June 16, 2025
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Shirin Yaƙi Da Yunwa na nan tafe

by DAGA WAKILIN MU
September 12, 2020
in Nijeriya
0
Hajiya Sadiya Umar Farouq

Hajiya Sadiya Umar Farouq

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram
Gwamnatin Tarayya ta na nan ta na ƙoƙarin fito da shirin Yaƙi Da Yunwa, wato Zero Hunger Round Table, don rage wa al’ummar Nijeriya raɗaɗin fatara da yunwa.
 
Ministar Harkokin Jinƙai, Agaji da Kyautata Rayuwar Al’umma, Hajiya Sadiya Umar Farouq, ita ce ta bayyana haka a wajen taron Cibiyar Samar Da Abinci ta Ƙasa (National Food Security Council) wanda aka yi a ranar Alhamis, 10 ga Satumba, a Fadar Shugaban Ƙasa da ke Abuja.
 
A jawabin da ta gabatar a taron, Hajiya Sadiya ta bayyana cewa za a fito da shirin ne a matsayin wani ɓangare ne na ƙoƙarin da ma’aikatar ke yi na rage yunwa a Nijeriya, wadda zaman dole na annobar korona ya ƙara kambamawa, da nufin kawar da yunwa tare da samar da abinci, inganta samar da abinci mai gina jiki da kuma haɓaka aikin gona ya zuwa shekara ta 2030 tare da haɗin gwiwar waɗanda abin ya shafa.
 
Ta ce: “Wannan Ma’aikatar ta samar da hanyoyin rage wa jama’a raɗaɗin matsalolin rayuwa ta hanyar samar da abinci cikin gaggawa da kuma hanya mai ɗorewa ta hanyar shirin Magance Yunwa.
 
“A matsayin ɗaya daga cikin ayyukan wannan Ma’aikata na tabbatar da rage raɗaɗin aukuwar bala’o’i tare da shirin ko-ta-kwana da kuma kai agaji, shirin Inganta Rayuwar Al’umma na Ƙasa (NSIPs) ya taimaka wa aikin Ma’aikatar a matsayin wata hanya ta samar da hanyoyin taimakon jama’a, ciki har da bada abinci ga mutane marasa galihu a dukkan faɗin ƙasar nan.”
 
Hajiya Sadiya Umar Farouq ta tuno da cewa shirin nan na ciyar da ‘yan makaranta da ke zaman gida da na kai abinci gida (Take Home Rations, THRs) an yi su ne domin samar da abinci ga gidaje mabuƙata guda 127,589 masu yara ‘yan aji 1 zuwa 3 na firamare a makarantun gwamnati a Yankin Babban Birnin Tarayya (FCT) da jihohin Legas da Ogun, yayin da aka kai manyan motoci 164 shaƙe da kayan abinci a jihohi 36 da yankin Abuja a matsayin agaji da aka samu daga Hukumar Kwastam ta Nijeriya.
 
Ta ƙara da cewa, “Ya zuwa yau dai, sama da tan 41,000 na hatsi daga Rumbunan Ajiyar Hatsi da ake sa ran za su kai ga gidaje sama da miliyan 5 aka miƙa wa gwamnatocin jihohi 19 da Babban Birnin Tarayya. Ana rabon ne ta hanyar hukumar NEMA a bisa umarnin Shugaban Ƙasa.”
 
Ministar ta ƙara da cewa Shirin Yaƙi Da Yunwa za a yi shi ne tare da haɗin gwiwar Ma’aikatar Aikin Gona da Haɓaka Karkara ta Tarayya  da kuma wasu shugabannin kamfanoni masu zaman kan su irin su Tony Elumelu, Tonye Cole da kuma Sahel Consulting, IFPRI, IITA, NESG, FAO, IMMAP, ECOWAS da sauran su.
 
Ta bayyana cewa hanyoyin da za a bi a aiwatar da wannan Shirin Yaƙi Da Yunwa ɗin sun haɗa da yin amfani da bayanan da aka tattara game da gidajen da ke buƙatar taimako, da haɗin gwiwa, samar da aikin yi da kuma taimaka wa sashen aikin gona tare da inganta hanyoyin da abinci ke bi daga manoma ya kai ga masu sayar da shi, da inganta samar da abinci mai gina jiki, ƙarfafa rumbunan tara abinci tare da haɗin gwiwar Ma’aikatar Aikin Gona da sauran masu ruwa da tsaki a lamarin.

Loading

Previous Post

Soyayyar mu da Fadila Ummi Lollipop ta har abada ce – Mala

Next Post

Zaɓen Edo: Za a hukunta masu laifi, inji shugaban INEC

Related Posts

Nijeriya tana kan hanyar farfaɗowar tattalin arziki da dawo da martabar ƙasa — Minista
Nijeriya

Nijeriya tana kan hanyar farfaɗowar tattalin arziki da dawo da martabar ƙasa — Minista

June 13, 2025
Gwamnatin Tarayya za ta tallafa wa yekuwar rigakafin cutar ƙyandar Jamus
Nijeriya

Gwamnatin Tarayya za ta tallafa wa yekuwar rigakafin cutar ƙyandar Jamus

June 4, 2025
Tinubu ya tura wakilai zuwa Neja kan ambaliyar Mokwa da ta halaka sama da mutum 150
Nijeriya

Tinubu ya tura wakilai zuwa Neja kan ambaliyar Mokwa da ta halaka sama da mutum 150

May 31, 2025
Gwamnatin Nijeriya ta goyi bayan amfani da Ƙirƙirarrar Basira cikin ɗa’a a aikin jarida – Idris
Nijeriya

Gwamnatin Tarayya ta yi ta’aziyyar mutanen da suka rasu a ambaliyar garin Mokwa

May 30, 2025
Babu wasu masu juya Tinubu ta bayan fage – Idris
Nijeriya

Babu wasu masu juya Tinubu ta bayan fage – Idris

May 25, 2025
Shirye-shiryen Shugaba Tinubu Suna Buɗe Hanyar Farfaɗowar Tattalin Arzikin Nijeriya – Idris
Nijeriya

Shirye-shiryen Shugaba Tinubu Suna Buɗe Hanyar Farfaɗowar Tattalin Arzikin Nijeriya – Idris

May 20, 2025
Next Post
Farfesa Mahmood Yakubu

Zaɓen Edo: Za a hukunta masu laifi, inji shugaban INEC

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!