• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Wednesday, June 4, 2025
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Shugaban Kadawood, Nura MC ya ƙalubalanci gwamnatin Kano kan hana yin fim ɗin daba

Ya ce hana yin fim kan daba ba zai hana harkar daba a Kano ba

by ABBA MUHAMMAD
April 7, 2024
in Labarai
0
Shugaban Kadawood, Nura MC ya ƙalubalanci gwamnatin Kano kan hana yin fim ɗin daba

Malam Nura MC Khan, Shugaban Kadawood

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

SHUGABAN ƙungiyar masu shirya finafinai ta Kadawood kuma sanannen jarumi, Malam Nura MC Khan, ya ƙalubalanci Hukumar Tace Finafinai da Ɗab’i ta Jihar Kano a game da hana shirya fim na daba da ta yi.

Nura MC, wanda mazaunin Kaduna ne, ya yi magana ne a ranar Laraba da ta gabata, jim kaɗan bayan da mujallar Fim ta buga labarin cewa Hukumar Tace Finafinai ta Jihar Kano ta haramta yin fim da harkar ‘yan daudu a jihar.

Ya ce, “Sai dai Alhaji Abba El-Mustapha ya manta cewa a YouTube ake kallon waɗannan finafinan da su ke tasiri a zukatan mutane, musamman matasa wanda su ka rasa mafaɗa a jihar.

“A nawa hangen, kusan an riga an makara in dai maganar daba ce a Jihar Kano ce. Ba wai kawai a fim ba ne su ke koya, kusan gadon sa aka yi in dai faɗan daba ne a Kano.

“Za mu iya tunawa tun ina ƙarami na ke jin ‘yan daban Yadakwari da menene ma sunan ɗayan? Na manta. To kun ga kuwa kusan ya zama jinin Kanawa.

“Idan El-Mustapha ya yarda da cewa a finafinai ne ake koyar da harkar daba, to babu ƙwarewa a wannan ɓangaren. Kuma with time mutane za su fara fito da matsaloli ɗaya bayan ɗaya su na danganta shi da fim, cewa ai a fim ake koyarwa.

“Wannan hanyar da hukumar ta ɗauka ba mai ɓullewa ba ce, domin wani aiki ne su ka ɗauko wa kan su wanda gaskiya, iya wannan kawai idan ya ɗauka har ya gama tenuwar sa ba zai iya samun cikakken nasara a kai ba.”

Haka kuma ya ƙara da cewa, “Kada su manta, akwai inda ake shirya finafinai wanda ba wai Kano ba ne kawai, shin ya za a yi da su?

“Ina da mafita wanda zan iya haska wa Hukumar Tace Finafinai, wataƙila ta yi tasiri. Amma hana nuna fim na daba, ba zai hana harkar daba a Kano ba.

“Ina goyon bayan hana nuna daudanci cikin finafinai, hakan kuma zai iya tasiri sosa ai ƙarƙashin hukumar.”

Idan kun tuna, a ranar Laraba ta makon jiya ne Hukumar Tace Finafinai ta Jihar Kano ta ba da sanarwar cewa ta soke shirya fim a kan harkar daba da kuma ‘yan daudu.

Jami’in yaɗa labarai na hukumar, Malam Abdullahi Sani Sulaiman, shi ne wanda ya ba sanarwar haka a wani saƙon manema labarai da ya fitar.

Ya ce, “Biyo bayan ƙorafe-ƙorafen da al’umma ke yi a kan shirya finafinan da ke nuna faɗan daba da harkar daudu a Jihar Kano, Shugaban Hukumar Tace finafinai da Ɗab’i ta Jihar Kano, Alhaji Abba El-Mustapha, ya ba da umarnin dakatarwa tare da hana dukkan finafinan da ke nuna faɗan daba da harkar daudu a faɗin Jihar Kano.”

Wannan hanin ya jawo ka-ce-na-ce a cikin jama’a, wasu na cewa ya yi daidai a yayin da wasu kuma ke cewa ai harkar daba da ta addabi jihar ba laifin ‘yan fim ba ne.

Loading

Tags: Abba El-MustaphaHukumar Tace Finafinai ta Jihar KanoKadawoodNura MC Khan
Previous Post

Haihuwa ta 13: Baba Ari ya samu Nana Khadija

Next Post

Jami’ar NOUN za ta ba Hafsatu Abdulwaheed da Innocent Chukwuma digirin girmamawa

Related Posts

An naɗa Shehu Hassan Kano shugaban riƙo na MOPPAN
Labarai

An naɗa Shehu Hassan Kano shugaban riƙo na MOPPAN

June 3, 2025
MOPPAN ta ba gwamnan Kebbi lambar yabo a madadin ‘yan fim
Labarai

MOPPAN ta ba gwamnan Kebbi lambar yabo a madadin ‘yan fim

June 2, 2025
Ƙungiya ta ja kunnen gwamnatin Kano kan dakatar da finafinan Kannywood 22
Labarai

Ƙungiya ta ja kunnen gwamnatin Kano kan dakatar da finafinan Kannywood 22

May 20, 2025
Hukuma ta rufe gidajen gala a Kano har sai bayan Ramadan
Labarai

Gwamnatin Kano ta dakatar da haska finafinan Kannywood 22 a intanet da talbijin 

May 19, 2025
Labarai

Gwamnan Kano ya ɗauki nauyin ‘yan Kannywood 5 zuwa Hajjin bana

April 17, 2025
Sabuwa, matar Ɗanmaraya Jos, ta rasu
Labarai

Sabuwa, matar Ɗanmaraya Jos, ta rasu

March 28, 2025
Next Post
Jami’ar NOUN za ta ba Hafsatu Abdulwaheed da Innocent Chukwuma digirin girmamawa

Jami'ar NOUN za ta ba Hafsatu Abdulwaheed da Innocent Chukwuma digirin girmamawa

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!