A YAU Juma’a jaruma kuma furodusa Hajiya Rahama Sadau ta yi wa mabiyan ta na Facebook mutum ɗari kyautar kuɗi don tallafawa kan halin matsi da ake ciki.
Tun da farko, jarumar ta rubuta cewa, “Barkan mu da Juma’a … Yau dai Let’s do some small giveaway, shall we? Drop Aza & I will pick randomly. Love Y’ll.”
Kafin ka ce kwabo, jama’a su ka yi caa su na tura lambar asusun bakin su a sashen sharhi (comment section) na shafin ta, wanda aƙalla an samu lambar asusun mutum sama da 23,800.
Bayan awa huɗu, Rahama ta rubuta cewa, “The target is to credit 100 people today with different amount. My hand don tire already. Please confirm receipt once you see alert. (I would also post receipts later). To be continued much later insha Allah. Till then, stay safe.”
Mujallar Fim ta fassara kamar haka, “Mutane ɗari ne hari na a yau da adadi mabambanta. Hannu na ya riga ya gaji. Don Allah ku aiko da rasit da zarar kun ga alat. Zan kuma buga rasit ɗin daga baya. Zan cigaba da ya daga baya in-sha Allah. Sai lokacin, ku zauna lafiya.”
Wasu daga cikin waɗanda su ka samu nasara sun fara tura rasiɗin kuɗin da Rahama ta tura masu.
A shekarun baya Rahama Sadau ita ce jarumar Kannywood da ta yi ƙaurin suna a soshiyal midiya, musamman idan ta yi abin da wasu ke ganin ba daidai ba ne.
Amma a yanzu jarumar ta na ɗaya daga cikin jaruman da ake yabo, musamman ganin ta daina saka ire-iren tufafin da ta ke sakawa masu nuna jikin ta.
A yau dai ta wanke kan ta, ta na ta shan ruwan addu’a wajen ɗimbin mutane, ana ta shi mata albarka.