TSOHON Shugaban Haɗaɗɗiyar Ƙungiyar Masu Shirya Finafinai ta Nijeriya (MOPPAN) na ƙasa, Alhaji Abdullahi Maikano Usman, ya bayyana irin jimamin da ya shiga na rashin Mubarak, ɗan aminin sa Alhaji Magaji Sulaiman da ya ke riƙo wanda ruwan Kogin Kaduna ya tafi da shi.
Idan kun tuna, mun ba ku labarin yadda a ranar Lahadi, 4 ga Disamba, 2022 Allah ya ɗauki ran Mubarak lokacin da ya je kogin a unguwar su, wato Kabala Costain, Kaduna, domin ya wanke ƙafar sa.
Mubarak, mai kimanin shekara 19 a duniya, shi ne babban ɗan matar Alhaji Magaji Sulaiman wadda mujallar Fim ta ba ku labarin rasuwar ta da ta faru a ranar Litinin, 22 ga Agusta, 2022, mai suna Hajiya Hannatu Yahaya.
Da ya ke zantawa da mujallar Fim kan wannan babban rashi da aka ƙara yi, Maikano ya ce, “Tsira da aminci su tabbata ga fiyayyen halitta, Annabi Muhammad (s.a.w.). A gaskiya, na yi jimamin rashin wannan ɗa nawa, Mubarak, domin yaro ne wanda ba shi da hayaniya, yaro mai ladabi da biyayya, wanda a gaskiya duk abin da na faɗa, ba ma ni kaɗai ba, a unguwar mu da jama’ar da ke tare da mu sun yi jimamin rasuwar wannan yaro.
“Yaro ne mai neman ilimi, yaro ne mai haƙuri, yaro ne mai son cigaba da neman ilimi, don a wancan satin mu ka gama tsari da makarantar da zan sa shi na haddar Alƙur’ani, amma ga shi Allah ya ɗauki abin sa. Wannan yaro ya yi shahada.
“Mu na roƙon Allah ya amshi shahadar sa, Allah ya ba mu haƙuri ga baki ɗaya, da ni mariƙin sa da mahaifin sa da al’ummar Annabi Muhammadu (s.a.w.), baki ɗaya.”

Maikano, wanda babban furodusa ne, ya bayyana wani abu da ke faruwa a kowane mako, ya ce, “A wannan Juma’ar da mu ke magana, hankali na a tashe ya ke, domin kowace Juma’a, haka na ke sanya su a gaba da sauran ‘ya’ya na, tun wurin ƙarfe 10:00 na safe, tun daga Kabala Costain za mu taka a ƙafa har masallacin Al-Manar, mu je mu zauna mu yi ta ibada, mu yi ta zikiri, har liman ya zo ya yi huɗuba, sannan mu dawo gida. Yau ita ce Juma’a ta farko da zan tafi Juma’a ba tare da Mubarak ba da sauran ‘ya’ya na a gaba ba.
“Ina roƙon Allah ya amshi shahadar sa, ya kuma gafarta masa, in tamu ta zo, Allah ya sa mu cika da kyau da imani.”
A labarin rasuwar Mubarak da mujallar Fim mujallar Fim ta buga, mahaifin marigayin, Alhaji Magaji Sulaiman, wanda shi ma babban furodusa ne da ke zaune a Zariya, ya shaida mana cewa ba a ga gawar yaron nasa ba. To Allah cikin ikon sa, a ranar Laraba, 7 ga Disamba, wato bayan kwana uku, aka ga gawar.
An yi masa sutura a gidan Maikano a nan Kabala, kuma Alhaji Magaji Sulaiman da ‘yan’uwan sa da ɗimbin jama’a sun halarta.
Allah ya jiƙan Mubarak, amin.