A YAU Lahadi, 19 ga Yuni, 2022 tsohuwar fitacciyar jaruma Fati Ladan da mijin ta Shettima Yerima su ka shirya gagarumin taron sunan ɗan da su ka haifa a cikin watan azumin Ramadana.
An yi taron a gidan su da ke Yerima Close, daura da Jinya Close da ke Titin Kanta, a Kaduna.
Idan ba ku manta ba, mujallar Fim ta ba ku labarin cewa Fati ta haifi ɗa namiji a safiyar Litinin, 11 ga Afrilu, 2022 a wani asibitin kuɗi da ke Unguwar Rimi, Kaduna.
Haka kuma a ranar Litinin, 18 ga Afrilu aka raɗa wa ɗan suna Muhammad Shafi’u, amma za a riƙa kiran sa da Amir saboda sunan mahaifin baban Shettima aka raɗa masa.

A yau an fara bikin sunan da misalin ƙarfe 3:38 na rana, bayan fitowar mai jego da ƙawayen ta da kuma Shettima da tawagar sa.
Bayan an buɗe da addu’a, sai aka kira jaruman barkwanci, Yabanya da Yaɗo, su ka nishaɗantar da mahalarta taron da wasannin su masu ƙayatarwa.
Ba a ɗauki tsawon lokaci ba aka fara raba abin sha, sannan aka biyo baya da abinci kala-kala. Duk wanda ya halarci taron sunan ya ci ya sha, ya gyatse.
A haka an ci gaba da nishaɗantar da taron inda Hussaini Danko, Jamila Sadi, Auwal Fresh da sauran mawaƙa su ka ci karen su ba babbaka.

Iyayenbjariri da sauran jama’a sun nuna farin cikin su a wannan rana, domin sun yi rawa sosai, kuma an yi masu kari.
Fitaccen jarumi Adam A. Zango shi ne ya nishaɗantar da taron har zuwa lokacin da aka tashi. Ya ɗauki kusan awa ɗaya ya na ɓarjewa da waƙoƙin sa.
Bikin ya ƙayatar, kuma ya samu halartar jama’a da dama daga sassa daban-daban na ƙasar nan, kasancewar dukkan su iyayen Muhammad Shafi’u masu jama’a ne.
Manyan mutane da dama sun halarci bikin sunan duk da yake wasun su ba su zauna ba.
‘Yan fim da su ka halarta sun haɗa da Yakubu Lere, Adam A. Zango, Jamilu Adamu Kochila, Hussaini Danko, Abubakar Hunter, Abdullahi Abbas, Nasir Aminu, Ɗanladiyo Mai Atamfa, A.A. Rasheed Kabala, Sadiya Gyale, Fauziyya Maikyau, Fati Macijiya, Fati KK, Jamila Sadi, Ummulkhairi Mukhtar, Rahama Sirace, Raliya Muhammad da sauran su.

A ƙarshe, Shettima ya gode wa dukkan waɗanda su ka halarci bikin, kuma ya yi wa addu’ar Allah ya maida koma gida lafiya.
An tashi daga bikin da misalin ƙarfe 6:45 na yamma.
Muhammad Shafi’u (Amir) shi ne ɗa na biyu da Fati ta haifa wa Yerima Shettima, wato har da Humaira. To Allah ya raya su baki ɗaya, amin.




