SHUGABAN kamfanin shirya fim na Jammaje Production, Kano, Malam Kabiru Musa Jammaje, ya yi kira ga dukkan wata mace mai so ta zama cikakkiyar jarumar fim da ta daina ƙunshi, musamman zanen fulawa a hannu da ƙafa, da kuma hujin hanci.
A cewar sa, hakan ne zai sa ta zama cikakkiyar jaruma.
A lokacin da yake ta’aliƙi a taron KILAF Awards 24 a makon da ya gabata, Jammaje ya ce: “Sau da dama sai ka ga mun tsara za mu fita aiki amma sai ka ga jarumai mata sun yi ƙunshin fulawa ko su zo da haƙorin Makka ko hujin hanci, wanda hakan yana shafar aikin mu, don wani lokacin ma har yana jawo mana asara saboda rol ɗin da za a ba su bai yi daidai da tsarin kwalliyar ta ba.
“Hakan zai sa ko dai a dakatar da sin ɗin da za ta hau zuwa lokaci da za ta sauya idan zai yiwu ko kuma a canza ta da wata, yayin da hakan yake jawo mana asara ta kuɗi da ta lokaci.
“Don haka in dai mace tana son ta zama cikakkiyar jaruma sai ta daina ƙunshi, musamman zanen fulawa da hujin hanci da saka haƙorin Makka.
“Ku duba yadda Nafisa Abdullahi take mana, saboda ta ɗauki fim sana’a kuma ta yarda ita jaruma ce, duk ba ta yin irin wannan abubuwan, don haka ba a samun matsala da ita a duk wani rol ɗin da za a ɗora ta ko na ƙauye ko na birni. Don haka ‘yan fim mata sai a rinƙa kulawa.”