HAUSAWA sun ce rana ba ta ƙarya, sai dai uwar ɗiya ta ji kunya. A yau Asabar, 11 ga Nuwamba, 2023 aka ɗaura auren jaruma a Kannywood, Hajiya Rashida Adamu Abdullahi (Maisa’a) da angon ta Alhaji Aliyu Adamu (Sardaunan Matasan Gwoza).
An ɗaura auren a layin Malam Bello da ke unguwar Daurawa, daura da babban Titin Maiduguri, a cikin birnin Kano.
Mujallar Fim ta ruwaito cewa ɗaurin auren ya samu halartar jama’a masu yawa.

Amarya Rashida ba ta shirya wani taron shagalin biki ba kamar yadda jaruman fim su ka saba yi, amma a jiya Juma’a an tara malamai a gidan ta da ke unguwar Na’ibawa a Titin Zariya, su ka wuni su na karatun Alƙur’ani.
Bayan haka da yamma an ɗan yi taron biki a ƙofar gidan, wanda ‘yan’uwa da abokan arziki su ka halarta domin taya ta murna.

‘Yan fim da su ka halarta sun haɗa da Asma’u Sani, Sadiya Gyale, Zahra’u Shata, Yahanasu Sani, Bilkisu Jibril, Maijidda Ibrahim, Fati Sulaiman, Saratu Giɗaɗo, Hadiza Kabara, Ruƙayya Dawayya, Hadiza Muhammad da Maryam Ceeter.
Allah ya bada zaman lafiya da ƙaruwar arziki.







