• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Friday, July 25, 2025
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Yadda na rasa ‘ya’ya na biyu a cikin motar da na yi fakin – Mawaƙi Sanusi Pambeguwa

by DAGA ABBA MUHAMMAD
October 4, 2021
in Labarai
0
Sanusi Pambeguwa da 'ya'yan sa da su ka rasu: Khaleed (a sama, mara hula) da Tasi'u (Khalifa).

Sanusi Pambeguwa da 'ya'yan sa da su ka rasu: Khaleed (a sama, mara hula) da Tasi'u (Khalifa).

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

MAWAƘIN nan Sanusi Ɗahiru, wanda aka fi sani da Sanusi Pambeguwa, ya yi bayani kan yadda ya gamu da ibtila’in rasuwar ‘ya’yan sa biyu a wani haɗari maras daɗin ji.

Mutuwar Khaleed da Tasi’u, yara ‘yan shekara biyar da haihuwa, ta faru ne jiya Lahadi, 3 ga Oktoba, 2021, a cikin motar sa da ya yi fakin a ƙofar gidan sa da ke garin Pambeguwa, a Ƙaramar Hukumar Kubau cikin Jihar Kaduna.

A lokacin da ya ke yi wa mujallar Fim bayani dalla-dalla game da yadda wannan abin baƙin ciki ya faru, Sanusi Pambeguwa ya ce, “Na dawo daga Zariya da misalin ƙarfe 11:30, mun yi taro a daren Asabar, na dawo gida Lahadi, na yi fakin mota ta a ƙofar gida. Yayan su sai ya zo ya karɓi biredin da ayaba da na sawo masu.

“Da su ka shiga gida sai su ka gan ni. Ni kuma da ma taron da mu ka yi na dare ne, bacci ya kama ni sosai, ban samu damar kwanciya da wuri ba. Ina zuwa, da na aje kaya sai na kwanta bacci. 

“Bayan an raba masu biredin, sai su ka fita waje. Sai ɗayan yaro na ya buɗe ƙofar motar, kamar yadda wani bawan Allah maƙwabcin mu na kusa da mu ya ke faɗa, yaron ya zo shagon mu ya na faɗa wa ɗan’uwan sa cewa, ‘Baban mu ya bar mota a buɗe, zo mu je mu shiga.’

“Allah cikin ikon sa, ina tunanin bayan sun shiga motar ne sai su ka danna wannan kilif ɗin, sai motar ta rufe baki ɗaya, kuma ban sauke gilashin motar ba. 

“Ni kuma saboda gajiya, ina kwanciya bacci ya ɗauke ni, ban tashi ba sai wurin ƙarfe 3:30 na yamma. 

“Bayan na tashi, na yi wanka na fita kasuwa. Da ma kuma ban sa a rai na zan sake fita da motar ba. 

“Daga baya, mata na su ka kira ni su ka ce mani ba a ga yara ba. Sai na ce masu ai yara za su ɓata ba, wataƙila sun bi ‘yan’uwan su zuwa makaranta ne. 

“Can daga baya, sai babban yaro na ya leƙa cikin motar, sai ya gan su, sai ya ke cewa ai ga su can a cikin mota su na bacci. 

“Allah da ikon sa, ana buɗe motar sai aka gan su sun rasu. Kuma an gano su a cikin motar ne da misalin ƙarfe 4:30 zuwa 5:00 na yamma. 

“Dukkan su ‘ya’ya na ne. Tsakanin su kwana bakwai; ranar sunan Khaleed aka haifi Tasi’u. Shekarun su huɗu zuwa biyar, ba su cika biyar ɗin ba. Mata na biyu, ‘ya’ya na goma.”

A binciken da mujallar Fim ta yi, ta gano cewa irin wannan haɗarin na yara su shiga mota ba a sani ba har su mutu ya na yawan faruwa a ƙasar nan.

Kwanan baya a Tudun Wada, Kaduna, ‘ya’yan wani mutum su ka shiga motar maƙwabcin su, su ka kasa fitowa, sai daga baya aka ga gawarwakin su a ciki bayan an sha cigiya.

A Kano a wata shekara kuma wani Inyamiri ɗan kasuwa ya bar motar sa ƙirar Baswaja a ƙofar gida, yaron maƙwabcin sa ya buɗe ya shiga, ya mutu a ciki ba a sani ba.

An yi ta neman yaron tsawon kwana biyu kafin a ji wani wari ya na fita daga cikin motar. Ana buɗewa, aka gan shi a kumbure a ciki.

Matasan unguwa sun so su kashe Inyamirin a bisa zargin wai matsafi ne, amma uban yaron da dattawan unguwa, waɗanda Hausawa ne, su ka hana domin Inyamirin mutumin kirki ne, har dai ‘yan sanda su ka zo su ka fitar da shi daga unguwar.

Ba kawai mota ba, wakilin mu ya gano cewa akwai abubuwa da dama da ke zama sanadiyyar rasa ran yara ƙanana. Misali, akwai wata yarinya da ta taɓa shiga cikin dif-firiza, aka neme ta sama da ƙasa ba a gan ta ba, kuma an ga takalman ta a bakin firiza ɗin amma babu wanda ya kawo a ran sa cewa ta na ciki. Sai daga baya da aka buɗe firizar aka gan ta a ciki har ta yi ƙanƙara.

Allah ya jiƙan Khaleed da Tasi’u da sauran shahidai irin su, ya sa masu ceton iyaye ne. Allah ya ba iyayen su haƙurin rashin su, amin.

Loading

Tags: hatsariKannywoodKubaumawakan hausamotamutuwaPambeguaSanusi Pambeguwa
Previous Post

Mai tallafa wa Kannywood, Farfesa Sule Bello, ya rasu

Next Post

Cewar Al-Amin Ciroma: Na yi mamaki da hamdala da mu ka cika shekara 19 da aure da Wasila Isma’il

Related Posts

‘Yan Kannywood sun kaɗu da rasuwar Abdoulfatah Omar
Labarai

‘Yan Kannywood sun kaɗu da rasuwar Abdoulfatah Omar

July 23, 2025
Allah ya yi wa mahaifiyar darakta Salisu Mu’azu rasuwa
Labarai

Allah ya yi wa mahaifiyar darakta Salisu Mu’azu rasuwa

July 17, 2025
Hukumar Shari’a da Hukumar Tace Finafinai za su haɗa gwiwa don tsaftace tarbiyya a Kano
Labarai

Hukumar Shari’a da Hukumar Tace Finafinai za su haɗa gwiwa don tsaftace tarbiyya a Kano

July 11, 2025
Jarumin Kannywood, Baba Ƙarami ya yi magana kan ganin sa da aka yi kan keken guragu 
Labarai

Jarumin Kannywood, Baba Ƙarami ya yi magana kan ganin sa da aka yi kan keken guragu 

July 10, 2025
Tsohuwar jarumar Kannywood, Halisa tana neman addu’a
Labarai

Tsohuwar jarumar Kannywood, Halisa tana neman addu’a

July 9, 2025
Mawaƙin Manzon Allah, Abdullahi Ɗan Gano ya rasu
Labarai

Mawaƙin Manzon Allah, Abdullahi Ɗan Gano ya rasu

July 7, 2025
Next Post
Al-Amin Ciroma da Wasila Isma'il

Cewar Al-Amin Ciroma: Na yi mamaki da hamdala da mu ka cika shekara 19 da aure da Wasila Isma'il

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!