FITACCEN jarumi kuma darakta a Kannywood, Al-Amin Ciroma, ya bayyana cewa ya yi mamaki tare da godiya ga Allah da aka faɗa masa cewa har sun cika shekara 19 da aure da fitacciyar jaruma Wasila Isma’il.
A bayanin da ya yi wa mujallar Fim, Ciroma ya ce, “Mamaki na yi sosai a daidai lokacin da aka faɗa min cewar har an cika waɗannan shekarun! Ta gefe ɗaya kuma sai mutum ya ce ikon Allah ne.”

Tun da safiyar wannan rana ta Laraba, 6 ga Oktoba, 2021 Hajiya Wasila ta wallafa hotunan su kwafe bakwai a Instagram, kuma ta rubuta haka da Turanci: “Happy 19th wedding anniversary to us. Alhamdu lillah ya Allah for the gift of life.”


Daga baya kuma, sai aka haɗa hotunan, aka ɗora waƙar fim ɗin ‘Wasila’, aka yi guntun bidiyo wanda shi ma ta ɗora shi a shafin nata.
Ɗimbin masoya sun taya ma’auratan murna.
A bayanin da ya yi wa Fim, Ciroma, wanda sanannen ɗan jarida ne, ya ƙara da cewa, “A yayin da wasu ke yi wa ‘yan fim kuɗin goro cewar ba sa yin haƙurin zaman aure, ga shi wasu su na cikar shekaru 19 da zaman auren.


“Babu shakka kuma tilas mutum ya yi wa Allah Ta’ala godiya, sannan a yi fatan duk matan da ke cikin masana’antar su ba maraɗa kunya.”
Allah ya ƙara haɗa kan su har tsawon rayuwar su, amin.
![]()







