FITACCEN daraktan finafinan Kannywood, Malam Aminu Saira, ya bayyana irin gudunmawar da matar sa ta farko, A’isha, ta bayar wajen gudanar da sabon auren sa da Maryam Mahmoud, yana mai cewa ita ce ta biya masa sadakin da kuɗin ta.
A wani saƙon godiya da ya wallafa a soshiyal midiya bayan an ɗaura auren sa da Maryam a garin Azare, Jihar Bauchi, daraktan ya ce Aisha ta nuna karamci da mutunci na musamman tun daga farkon shirin auren, ciki har da biyan sadakin Maryam da kuɗin ta da kuma bayar da gudunmawa a sauran harkokin bikin.
Saira ya ce hakan da ta yi ya ƙara mata daraja a idanun sa da kuma na iyalan amaryar.
Ya ce, “Karamci, mutunci da sadaukarwa na ƙarshen ƙurewa uwargida na Aisha ta nuna a cikin hidimar aure na.”
Ya ƙara da cewa Aisha ba wai kawai ta taimaka wajen gudanar da bikin ba ne, har ma ta karɓi sabuwar abokiyar zaman ta cikin girmamawa da kyakkyawar mu’amala.
“Wannan ya ƙara mata ƙololuwar daraja a idanu na da idon amarya ta da dangin ta. Mace irin Aisha, babu wani ɗan halak da ba zai mata adalci da halacci ba,” inji shi.
Saira ya kuma bayyana dalilin da ya sa ya zaɓi Maryam Mahmoud a matsayin sabuwar matar sa, yana mai cewa ta nuna halayen nagarta tun daga farkon al’amuran auren su.
“Na auri Maryam saboda tana da halayen nagarta na ƙarshe ita ma, kuma su ta yi ta nunawa tun daga farkon al’amari,” inji daraktan.
Ya ce ya gode wa Allah da ya azurta shi da matan sa, yana fatan za su ci gaba da tafiya a kan hanya madaidaiciya.
A wani saƙon godiya da ya wallafa, Saira ya gode wa ’yan’uwa da abokan arziki da suka halarci bikin auren a Azare, da kuma waɗanda ba su samu damar zuwa ba amma suka taya shi da iyalan sa da addu’o’i.
Ya ce, “Ina miƙa saƙon godiya ga ’yan’uwa da abokan arziki da suka halarci bikin aure na a garin Azare da ke Jihar Bauchi, sannan ina miƙa godiya ga mutanen da ba su samu damar halarta ba, suka taya mu da addu’a.”
Daraktan ya bayyana cewa babban abin da yake fata shi ne samun ikon gudanar da rayuwar auren sa bisa adalci da koyarwar addini.
“Mu kuma Allah ya ba mu ikon yin adalci ga matan mu kamar yadda addinin mu ya yi umurni,” inji shi.
![]()






