‘YA’YA biyu mata na fitaccen mawaƙi a Kannywood, Malam Muddassir Ƙassim, wato Fatima da Zainab, sun yi saukar Alƙur’ani Mai Tsarki.
An gudanar da bikin saukar a yau Lahadi a makarantar su, Madarasatul Murattilul Qur’an Al-Islamiyya, da ke unguwar Ɗorayi Babba, a cikin Ƙaramar Hukumar Gwale, Kano.
’Yan’uwa, abokan arziki da sauran al’umma da dama sun halarci taron domin taya Fatima da Zainab murnar wannan gagarumar nasara tare da yi masu fatan alheri.

Haka kuma mahalarta taron sun yi addu’ar Allah ya sanya albarka cikin ilimin Alƙur’ani da suka samu, ya ba su ikon amfani da shi a rayuwar su, tare da zama sanadin alheri a duniya da lahira.
![]()







