SHIRYE-SHIRYE sun yi nisa domin gudanar da babban taron gabatar da littafin waƙoƙi mai suna ‘Tambarin Zamani’, wanda fitacciyar mawaƙiya Salma Sa’eed Mailambu ta rubuta.
Za a gudanar da taron a ranar Asabar mai zuwa, 29 ga Agusta, 2026 a ɗakin taro na Gidan Mambayya da ke Gwammaja, Kano.
Ana sa ran taron zai samu halartar manyan baƙi daga sassa daban-daban na ƙasar nan, musamman malamai, ɗalibai da masu nazarin adabi da al’adun Hausawa.
Salma, ƙaramar yarinya ce wadda mutane suke yi wa laƙabi da ‘yar baiwa saboda ganin irin basirar da Allah ya ba ta.
‘Ya ce ga shahararriyar marubuciyar nan, Hajiya Halima K Mashi.
Ta yi fice wajen gabatar da waƙoƙi a soshiyal midiya, waɗanda suka haɗa da bitar waƙoƙin fitattun makaɗan Hausa da kuma waɗanda ta rubuta da kan ta.
Littafin Tambarin Zamani ya ƙunshi waƙoƙi 20 daga cikin fitattun waƙoƙin da ta rubuta, aka tattara aka mayar da su cikin littafi domin ƙara bunƙasa harkar adabi tare da samar da wata hanya ta adana waƙoƙin ga al’umma.
Littafin ya samu bitar masana, tare da gyare-gyare da ingantawa daga wasu fitattun masana a fannin adabi da ilimi, ciki har da Dakta Ibrahim Sheme na Jami’ar Buɗaɗɗiyar Nijeriya (NOUN), Dakta Murtala Uba na Jami’ar Bayero, Kano (BUK), da Dakta Mujahid na Jami’ar Jihar Kaduna.
Ana kallon gabatar da littafin a matsayin wani muhimmin mataki wajen bunƙasa adabin Hausa da adana gudunmawar mawaƙan zamani ga al’adu da tarihin al’ummar Hausawa.
Salma, wadda mutane suke yi wa laƙabi da ‘yar baiwa, ‘ya ce ga shahararriyar marubuciyar nan, Hajiya Halima K Mashi.
![]()





