• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Wednesday, May 6, 2026
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Zaɓen Anambra: INEC za ta raba kayan aiki marasa hatsari daga Owerri

by DAGA WAKILIN MU
September 8, 2021
in Nijeriya
0
Zaɓen Anambra: INEC za ta raba kayan aiki marasa hatsari daga Owerri
0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

HUKUMAR Zaɓe ta Ƙasa (INEC) ta ce za ta yi amfani da hedikwatar ta ta yanki da ke Owerri wajen rarraba kayan aiki marasa hatsari na zaɓen gwamnan Jihar Anambra da za a yi.

Shugaban INEC, Farfesa Mahmood Yakubu, shi ne ya bayyana haka a wajen taron bayan wata huɗu da ya kan yi da manyan ‘yan jarida, wanda aka yi a Abuja a ranar Laraba ta wannan makon.

Farfesa Yakubu ya ce an yanke shawarar yin haka ne sakamakon hare-haren da aka kai tare da lalata kayan hukuma a Anambra kwanan nan.

Ya ce kayan aikin zaɓen waɗanda ba su da hatsari su ne za a raba daga ofishin yanki na INEC da ke Owerri zuwa ofisoshin ta na ƙananan hukumomi da ke Anambra.

Ya kuma bayyana jin daɗin ganin cewa hukumar ba ta samu wani sabon hari ba a kan kayayyakin ta tun daga watan Yuni.

Babban Kwamishinan INEC, Farfesa Okechukwu Ibeanu, shi ma ya yi jawabi, inda ya ce yin amfani da ofishin yanki da ke Owerri ya zama tilas domin hukumar ba ta gama wattsakewa sosai ba daga hare-haren da aka kai wa kayayyakin ta a kwanan baya a jihar.

Ibeanu, wanda kuma shi ne shugaban Kwamitin Gudanar da Zaɓe da Kayan Aiki (Electoral Operations and Logistics  Committee, EOLC), ya ce sama da kashi 50 cikin ɗari na kayan aiki maras hatsari da aka riga aka tara ne aka lalata a lokacin waɗancan hare-haren.

To amma, a cewar sa, INEC ta tattaro kayayyaki marasa hatsari da ake buƙata, waɗanda su ka haɗa da rumfunan kaɗa ƙuri’a, daga sauran jihohin ƙasar nan. 

Ya ce duk da yake an samu cigaba wajen kyawawan hanyoyin mota a Anambra, hukumar ta na kammala shirye-shirye don a rarraba kayan zaɓe da kwale-kwale a yankuna masu yawan rafuka a jihar.

Ya ƙara da cewa hukumar za kuma ta yi amfani da wata manhaja a komfuta wajen sa ido kan aikin rarraba kayan.

Da ya ke bayyana damuwa kan yanayin tsaro a Anambra, Ibeanu ya ce hukumar na yin aiki tare da hukumomin tsaro don tabbatar da an samar da irin tsaron da ake buƙata a zaɓen da za a yi a jihar.

Ya kuma bayyana cewa hukumar ta na buƙatar ma’aikatan wucin gadi kimanin mutum 25,000 da za su gudanar da zaɓen jihar.

Wajen amsa wata tambaya, Ibeanu ya yi watsi da cewa ‘yancin da INEC ta ke da shi a ƙarƙashin kundin tsarin mulki ya sa ta na ɗaukar umarni daga Hukumar Sadarwa ta Nijeriya (NCC) wajen tura sakamakon zaɓe a matsayin abin da ya saɓa wa tsarin mulki.

Ya ce ta hanyar yin aiki da tsarin mulki, hukumar ta na da ƙarfin yin amfani da ikon ta, to amma idan abin ya shafi sanya wani ma’aikacin gwamnatin tarayya ya yi wani aiki to sai shugaban ƙasa ya amince.

Ya ce, “Bari kuma in alaƙanta wannan da shawarar da Majalisar Tarayya ta bayar cewa idan har za a tura sakamakon zaɓe ta intanet, tilas ne INEC ta samu amincewar NCC, ya ce hakan ya yi matuƙar saɓa wa tsarin mulki.

“Ba za mu iya cewa idan INEC za ta tura sakamakon zaɓe sai ta samu amincewar wata hukumar gwamnati ta daban bayan kuma ita INEC ɗin ta na da ikon ta sanya NCC ta cimma nasarar tura sakamakon zaɓen.

“Saboda haka, ni abin da na fahimta kenan da Sashe na Section 162 na Kundin Tsarin Mulki. Na amince da ku ɗari bisa ɗari a kan batun tabbatar da ‘yancin INEC, Sashe na 162 ya kammala komai da ke buƙatar a yi shi.

“Abin da ya rage wa INEC shi ne ta yi amfani da ikon da tsarin mulki ya ba ta.”

Loading

Tags: Anambra electionINECProf. Mahmood YakubuProf. Okechukwu Ibeanu
Previous Post

Karatun boko ko na allo: Mu tashi mu farka

Next Post

An yi finafinai 635 a Nijeriya a kwata ta biyu ta 2021, inji gwamnati

Related Posts

Yadda CBN ke tallabe da tattalin arzikin Nijeriya, yayin sa farashin ɗanyen mai ke faɗuwar-‘yan-bori a kasuwa
Nijeriya

Yadda CBN ke tallabe da tattalin arzikin Nijeriya, yayin sa farashin ɗanyen mai ke faɗuwar-‘yan-bori a kasuwa

November 7, 2025
Shirin ƙarfafa jari: CBN ya shawarci bankuna marasa ƙarfi su haɗe ko su rage wa lasisin su geji
Nijeriya

Shirin ƙarfafa jari: CBN ya shawarci bankuna marasa ƙarfi su haɗe ko su rage wa lasisin su geji

November 2, 2025
Bankin CBN ya yunƙuro: Naira ta hana dala numfashi mai ƙarfi a ƙarshen Oktoba
Nijeriya

Bankin CBN ya yunƙuro: Naira ta hana dala numfashi mai ƙarfi a ƙarshen Oktoba

November 2, 2025
Bankin CBN ya ƙaryata ƙazafin sayar wa manyan dillalan mai dala biliyan 1.259 domin su shigo da fetur daga waje
Nijeriya

Bankin CBN ya ƙaryata ƙazafin sayar wa manyan dillalan mai dala biliyan 1.259 domin su shigo da fetur daga waje

October 29, 2025
Tinubu ya yi adalci ga dukkan yankunan Nijeriya – Ministan Yaɗa Labarai
Nijeriya

Tinubu ya yi adalci ga dukkan yankunan Nijeriya – Ministan Yaɗa Labarai

August 31, 2025
Nijeriya

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar da Sababbin Cibiyoyin Maganin Ciwon Daji

July 24, 2025
Next Post
An yi finafinai 635 a Nijeriya a kwata ta biyu ta 2021, inji gwamnati

An yi finafinai 635 a Nijeriya a kwata ta biyu ta 2021, inji gwamnati

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!