• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Wednesday, May 6, 2026
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Za a yi Babban Zaɓen 2023 a ranar 18 ga Fabrairu – INEC

by DAGA WAKILIN MU
April 28, 2021
in Nijeriya
0
Za a yi Babban Zaɓen 2023 a ranar  18 ga Fabrairu – INEC
0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

HUKUMAR Zaɓe ta Ƙasa (INEC) ta bayyana cewa a ranar 18 ga Fabrairu ne za a gudanar da Babban Zaɓen shekarar 2023.

Shugaban INEC, Farfesa Mahmood Yakubu, shi ne ya bayyana haka a ranar Laraba a cikin jawabin da ya gabatar wajen taron dandalin sauraron jama’a a kan Ƙudirin ƙirƙiro Dokar kafa Hukumar Hukunta Laifuffukan Zaɓe ta Ƙasa wanda Kwamitin Hukumar Zaɓe na Majalisar Dattawa ya shirya a Abuja.

Farfesa Yakubu ya ce: “Wannan Hukuma ta ƙosa ta san irin dokar da za ta yi aiki da ita wajen aiwatar da  manyan zaɓuɓɓukan shekarar 2023. A bisa ƙa’idojin da Hukumar ta kafa, za a gudanar da manyan zaɓuɓɓukan 2023 ne a ranar Asabar, 18 ga Fabrairu, 2023, wanda ya kama shekara ɗaya da wata tara da mako biyu da kwana shida daidai daga yau ɗin nan ko kwanaki 660.”

Shugaban ya ce shekaru 13 bayan shawarar da Mai Shari’a Muhammadu Lawal Uwais ya bayar kan a kafa Hukumar Hukunta Laifuffukan Zaɓe (National Electoral Offences Commission), da kuma wasu rahotannin kwamitoci daban-daban a kan batun, “a yau ga mu a wajen wannan taro na tarihi domin mu bada namu shawarwarin kan wannan doka.”

Ya ce, “Ba shakka, an ɗora wa INEC ayyuka masu yawa domin ana yin zaɓuɓɓuka a sassan Nijeriya a duk tsawon shekara.

“Tun daga zaɓen 2015, an gudanar da shari’u 124 kan laifuffukan zaɓe amma a guda 60 kaɗai ne aka yanke hukunci.”

Ya ƙara da cewa: “To amma, a yayin da mu ke jin daɗi game da wannan taron na yau, mu na kuma so a fito da tsarin doka mai suna Dokar Zaɓe (Gyararriya) wanda a kan ta za a aiwatar da zaɓuɓɓukan 2023, wanda za a yi a ranar 28 ga Fabrairu, 2023, kuma a rattaba hannu a kan ta a kan lokaci.”

Tun da fari, sai da Shugaban Kwamitin Hukumar Zaɓe na Majalisar Dattawa, Sanata Kabiru Gaya, ya bada tabbaci ga dukkan masu ruwa da tsaki cewa Ƙudirin Dokar Zaɓe (Gyararriya) na 2021 ya na samun kulawa kuma ana fatan Shugaban Ƙasa zai rattaba hannu a kan ta.

Gaya ya ce ba shakka kafa Hukumar Hukunta Laifuffukan Zaɓe ta Ƙasa “zai canza labarin tsarin mu na gudanar da zaɓe.”

Wanda ya kawo ƙudirin kafa Hukumar Hukunta Laifuffukan Zaɓe ta Ƙasa, Sanata Abubakar Kyari, ya ce an fara ƙudirin kafa hukumar ne tun a Majalisar Dattawa ta 8 lokacin da ya kawo shawarar ƙudirin tare da Ovie Omo-Agege saboda sun fahimci cewa INEC ba ta iya hukunta ko da kashi 1 cikin ɗari na laifuffukan zaɓe, saboda haka akwai buƙatar a ɗauke wannan aikin daga kafaɗun ta, a bar ta ta yi aikin ta da kyau.

Loading

Tags: 2023 General ElectionsElectoral ActINECNational Electoral Offences CommissionNigeria electionsProf. Mahmood YakubuSenator Kabiru Gaya
Previous Post

‘Sirrin Ɓoye’: Hatsabibiyar yarinya a Kannywood

Next Post

Rasuwar mahaifiyar Sarkin Kano rashi ne gare mu, inji ‘yan Kannywood

Related Posts

Yadda CBN ke tallabe da tattalin arzikin Nijeriya, yayin sa farashin ɗanyen mai ke faɗuwar-‘yan-bori a kasuwa
Nijeriya

Yadda CBN ke tallabe da tattalin arzikin Nijeriya, yayin sa farashin ɗanyen mai ke faɗuwar-‘yan-bori a kasuwa

November 7, 2025
Shirin ƙarfafa jari: CBN ya shawarci bankuna marasa ƙarfi su haɗe ko su rage wa lasisin su geji
Nijeriya

Shirin ƙarfafa jari: CBN ya shawarci bankuna marasa ƙarfi su haɗe ko su rage wa lasisin su geji

November 2, 2025
Bankin CBN ya yunƙuro: Naira ta hana dala numfashi mai ƙarfi a ƙarshen Oktoba
Nijeriya

Bankin CBN ya yunƙuro: Naira ta hana dala numfashi mai ƙarfi a ƙarshen Oktoba

November 2, 2025
Bankin CBN ya ƙaryata ƙazafin sayar wa manyan dillalan mai dala biliyan 1.259 domin su shigo da fetur daga waje
Nijeriya

Bankin CBN ya ƙaryata ƙazafin sayar wa manyan dillalan mai dala biliyan 1.259 domin su shigo da fetur daga waje

October 29, 2025
Tinubu ya yi adalci ga dukkan yankunan Nijeriya – Ministan Yaɗa Labarai
Nijeriya

Tinubu ya yi adalci ga dukkan yankunan Nijeriya – Ministan Yaɗa Labarai

August 31, 2025
Nijeriya

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar da Sababbin Cibiyoyin Maganin Ciwon Daji

July 24, 2025
Next Post
Rasuwar mahaifiyar Sarkin Kano rashi ne gare mu, inji ‘yan Kannywood

Rasuwar mahaifiyar Sarkin Kano rashi ne gare mu, inji 'yan Kannywood

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!