• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Thursday, May 14, 2026
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Zaɓen Edo: INEC da jami’an tsaro sun kyauta – Gwamna Wike

by DAGA WAKILIN MU
September 20, 2020
in Nijeriya
0
Gwamnan Jihar Ribas, Ezenwo Nyesom Wike

Gwamnan Jihar Ribas, Ezenwo Nyesom Wike

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram
GWAMNAN Jihar Ribas, Mista Nyesom Wike, ya yaba wa Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC) da hukumomin tsaro kan yadda aka gudanar da zaɓen gwamna na Jihar Edo a ranar Asabar cikin lumana.
 
Wike, wanda ya na daga cikin ‘yan sa ido a zaɓen, kuma ɗan jam’iyyar PDP ne, ya yi wannan tsokacin ne a lokacin da ya ke zantawa da ‘yan jarida a Gidan Gwamnati da ke Benin, babban birnin jihar.
 
Ya ce: “Yanzu ni dai ba ni da ikon bayyana sakamakon zaɓen, to amma daga rahotannin da mu ke samu zuwa yanzu daga wuraren da aka yi zaɓen, ina tsammanin dai mu na farin ciki.  
 
“Ina so in yaba wa INEC zuwa yanzu saboda yadda su ka tabbatar da cewa jama’a sun kaɗa ƙuri’un su a rumfunan zaɓe daban-daban.
 
“Ina kuma yaba wa hukumomin tsaro zuwa yanzu saboda yadda su ka tabbatar da cewa babu hatsaniya sosai, kuma idan aka ci gaba a haka ina tsammanin wani cigaba ne.
 
“Shi zaɓe, wani abu ne da ake yi mataki-mataki, ba a kai ga tattaro sakamakon ba tukuna; sai an tattaro sakamakon sannan za mu iya bada ra’ayin mu na ƙarshe.
 
“Zuwa yanzu dai, zan iya cewa sun yi daidai.
 
“Abin da mu ke cewa shi ne su tsaya tsayin daka kan abin da ya faru, kuma INEC ta tabbatar da cewa kada wani ya yi ƙoƙarin canza abin da mutane su ka zaɓa wa kan su; abin da mu ke cewa kenan. Idan jam’iyyar APC ce ta lashe zaɓen to a bar shi a haka. Idan kuma PDP ce ta lashe zaɓen, to shi ma a bar shi a haka.
 
“Ina dai jin mun ji daɗin abin da ya wakana yanzu. Ina jin yanzu mu na da rumfunan zaɓe sama da guda 2, 000.
 
“Ina jin mu na farin ciki sosai kuma idan aka ci gaba a haka wannan zaɓe zai kasance ɗaya daga cikin mafi inganci da za a ce mun gani a Nijeriya.
 
“Ba wai kawai batun kaɗa ƙuri’a ba ne. Bayan kaɗa ƙuri’a, ana ƙirga ƙuri’u, daga nan sai a tafi haɗa sakamako.
 
“Wannan shi ne mataki mai matuƙar muhimmanci, kuma lallai ne su tsare cibiyoyin su na tattaro sakamako daga matakin unguwa zuwa matakin ƙaramar hukuma har zuwa matakin jiha saboda duk wanda ya yi zaɓe zai ji daɗin cewa buƙatar sa ta biya.”
 
A game da labarin da aka riƙa yaɗawa cewa sama da ‘yan sanda 300 sun kai masa farmaki a ɗakin sa na otal a garin Benin a ranar Juma’a, Gwamna Wike ya ce yanzu dai wannan lamari ya zama tarihi.
 
“Abin da ya faru jiya ya riga ya faru; yanzu kun gan ni, ban bar Edo ba,” inji shi.

Loading

Previous Post

Saƙon Shugaban INEC Kan Zaɓen Edo

Next Post

PDP ta lashe zaɓen Edo, an yaba wa INEC

Related Posts

Yadda CBN ke tallabe da tattalin arzikin Nijeriya, yayin sa farashin ɗanyen mai ke faɗuwar-‘yan-bori a kasuwa
Nijeriya

Yadda CBN ke tallabe da tattalin arzikin Nijeriya, yayin sa farashin ɗanyen mai ke faɗuwar-‘yan-bori a kasuwa

November 7, 2025
Shirin ƙarfafa jari: CBN ya shawarci bankuna marasa ƙarfi su haɗe ko su rage wa lasisin su geji
Nijeriya

Shirin ƙarfafa jari: CBN ya shawarci bankuna marasa ƙarfi su haɗe ko su rage wa lasisin su geji

November 2, 2025
Bankin CBN ya yunƙuro: Naira ta hana dala numfashi mai ƙarfi a ƙarshen Oktoba
Nijeriya

Bankin CBN ya yunƙuro: Naira ta hana dala numfashi mai ƙarfi a ƙarshen Oktoba

November 2, 2025
Bankin CBN ya ƙaryata ƙazafin sayar wa manyan dillalan mai dala biliyan 1.259 domin su shigo da fetur daga waje
Nijeriya

Bankin CBN ya ƙaryata ƙazafin sayar wa manyan dillalan mai dala biliyan 1.259 domin su shigo da fetur daga waje

October 29, 2025
Tinubu ya yi adalci ga dukkan yankunan Nijeriya – Ministan Yaɗa Labarai
Nijeriya

Tinubu ya yi adalci ga dukkan yankunan Nijeriya – Ministan Yaɗa Labarai

August 31, 2025
Nijeriya

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar da Sababbin Cibiyoyin Maganin Ciwon Daji

July 24, 2025
Next Post
Gwamna Godwin Obaseki

PDP ta lashe zaɓen Edo, an yaba wa INEC

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!