LAUYOYIN jarumi kuma mawaƙi a Kannywood,
Abdullahi Ɗan’azumi (Amdaz) a yau sun aika da martani a rubuce ga lauyoyin furodusa Mustapha Ahmad (Alhaji Sheshe), wanda a jiya Alhamis ya yi barazanar zai maka jarumin a kotu kan kalaman da ya yi dangane da ayyukan assha da ya yi iƙirarin ana aikatawa a masana’antar.
Idan kun tuna, jarumin ya furta kakkausan zargin ne a jawabin da ya gabatar a wurin taron da Hukumar Hisbah ta Jihar Kano ta yi da ‘yan fim a ranar Litinin da ta gabata.
Kalaman nasa sun dugunzuma wasu daga cikin ‘yan fim, yayin da wasu kuwa su ke mara masa baya.
Alhaji Sheshe ya na ɗaya daga cikin ‘yan fim da jawabin ya yi wa ciwo, wanda ya sa a jiya Alhamis ya sanya lauyoyin sa su ka rubuta wa Amdaz takardar barazanar cewa ko dai ya janye kalaman sa ko kuma su maka shi a kotu.
To a yau a soshiyal midiya sai Amdaz ya wallafa shafin takardar da lauyoyin sa su ka aika wa da na Alhaji Sheshe.
A takardar falle ɗaya wadda mujallar Fim ta gani, lauyoyin, masu kamfanin ‘Humanity Associates’ da ke da adireshi a Sharaɗa, Kano, sun ce sun sadu da takardar da aka rubuta wa wanda su ke wakilta, wato Amdaz, kuma shi ne ya ba su umurnin su maida amsa.
Mujallar Fim ta fassara takardar tasu kamar haka: “Duk da yake mu na so mu ba ku amsa cikakkiya kan wasiƙar ku, amma mu na so ku fara da ba mu bayanai kan wasu abubuwa da mu ka lura da su a nan domin kada mu je mu na ɓata lokacin mu wajen musayar magana da wasu da ke yaudara da cewar su lauyoyi ne.
“Na farko, bincike a gurguje a gidan yanar hukumar CAC bai nuna akwai wani kamfani ko wani bayani da aka shigar ba kan ‘N & N Attorneys ‘, wanda hakan ya haifar da damuwa kan idan da gaske akwai wani kamfani da aka yi wa rajista da wannan sunan wanda mu ke magana da shi.
“Na biyu, an yi amfani da hatimin da ya daina aiki na wani mai suna Uba Nazeer Abdullahi, a yayin da ita wasiƙar ke ɗauke da sa-hannun wani mai suna Cif Nnamdi Onana tare da wasu.
“Na uku, a kan batun da ake magana, mu na ba ku shawarar ku samu cikakken kwafen jawabin na sauti, a rubuta shi a rubuce kuma a samu ƙwararriyar fassarar shi daga sauti, wato wanda ku ka ɗora zargin ku a kai, sannan ku faɗi daidai ainihin wurin da aka ambaci sunan wanda ku ke wakilta kafin ku yi iƙirarin cewa wanda mu ke wakilta ya yi ‘maganganu babu tunani, masu ɗauke da ɓatanci da kuma tozarci’ ga wanda ku ke wakilta.

“Mun yi amanna da cewa babu wani lauya da ya amsa sunan sa wanda zai ɗauki kalaman wanda mu ke wakilta a matsayin ɓatanci ga kowane mutum sai idan shi mutumin…”
A daidai nan shafin wasiƙar da Amdaz ya wallafa ta ƙare, mujallar Fim ba ta samu kwafen shafi na biyu ba don ganin cigaban bayanan lauyan nasa.
Tun daga lokacin da wannan ƙurar da ta tashi, Amdaz ya fito a jiya ya bayyana cewa ya na fuskantar barazana ga rayuwar sa. Ya ce: “Ana yi wa rayuwa ta barazana saboda na faɗi gaskiya a kan abin da ya ke faruwa a Kannywood.”
Amma bai yi bayani a kan haka ba. Sai dai a wata sanarwa da ya fitar a jiya ɗin, ya ce ba zai taɓa bada haƙuri ba kamar yadda lauyoyin Alhaji Sheshe su ka buƙace shi da ya yi.
Ya ce: “Na karɓi sammacin kotu, amma har Mahdy ya bayyana a busa ƙaho ba zan ƙaryata kai na ba. Kuma zan bi wannan takarda da Hasbunallahu wa ni’imal wakeel, amma dai daga yanzu har Mahdi ya bayyana a busa ƙaho ban ga kotu ko wani ɗan’adam da ya isa ya saka ni ƙaryata kai na ba.”
Amdaz ya ƙara da cewa, “Ba sa’o’i 48 ba, har zaren agogo ya tsinke babu wanda ya isa ya sa ni ba da haƙuri a cikin haƙƙin Ubangiji, don haka duk abin da na faɗa na faɗa, ba zan ƙaryata kai na ba a kan wannan maganar.
“Tunda kun kasa kawo hujja ko ƙaryata abin da na faɗa, kawai ku karɓi gaskiya ku huta, ku yi umarni da kyakykyawa ku yi hani da mummuna.”
Jama’a dai a yanzu sun zuba ido su ga yadda wannan turka-turkar za ta kaya.