• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Tuesday, July 15, 2025
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Mahaifin Rahama Sadau mutumin kirki ne da son jama’a, inji Yerima Shettima

by ABBA MUHAMMAD
June 22, 2025
in Labarai
0
Mahaifin Rahama Sadau mutumin kirki ne da son jama’a, inji Yerima Shettima

Alhaji Yerima Shettima kusa da Rahama Sadau a lokacin da ake addu'a

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

Shugaban Ƙungiyar Tuntuɓa ta Matasan Arewa (AYCF) na ƙasa, Alhaji Yerima Usman Shettima, ya bayyana mahaifin Rahama Sadau a matsayin mutumin kirki, mai son jama’a.

Yerima, wanda shi ne mijin tsohuwar jarumar Kannywood Fati Ladan, ya yi wannan bayani ne a lokacin da ya je ta’aziyya gidan marigayin, wato marigayi Alhaji Ibrahim Sadau.

Shugaban ya shaida wa mujallar Fim cewa, “Haƙiƙa duk wanda ya san Alhaji Ibrahim Sadau, ya san cewa mutum ne mai kirki da son jama’a. Ko da na wannan wuri na ƙara tabbatar da haka.

“Babu abin da ya kamata mu yi masa a yanzu da ya wuce addu’ar neman gafara da rahama a gare shi.”

Ya ƙara da cewa, “Muna kuma fatan halayen sa na kirki su bi shi. Allah ya yafe masa kurakuran sa, Allah ya albarkaci dukkan zuri’ar sa.”

Shettima a yayin da suke addu’a tare da mahaifiyar su Rahama, wato Hajiya Bilkisu
Yerima a cikin ‘yan’uwan marigayi Alhaji Ibrahim Sadau suna addu’a

Yerima da tawagar sa sun isa gidan su Rahama da misalin ƙarfe 5:00 na yamma, inda kai-tsaye aka yi masu jagora zuwa inda Rahama take.

An gudanar da addu’o’in neman gafara ga mamacin, wadda Malam Ibrahim PDP ya jagoranta.

Haka kuma sun shiga cikin falon da Hajiya Bilkisu, wato mahaifiyar su Rahama take, sun yi mata ta’aziyya tare da yin addu’o’i.

Daga nan kuma suka fita waje inda ‘yan’uwan mamacin suke, nan ma suka yi masu gaisuwa da addu’a.

Rahama da ‘yan’uwan ta sun yi wa su Yerima godiya da fatan Allah ya maida su gida lafiya.

Loading

Tags: Alhaji Ibrahim SadauRahama Sadaurasuwar mahaifita'aziyyaYerima Shettima
Previous Post

Yadda mahaifin mu ya rasu kwana ɗaya bayan ya dawo daga Makkah – Abba, yayan Rahama Sadau

Next Post

Ƙungiyoyin harkar fim, KAFIGAN da MOPPAN, sun yi wa Rahama Sadau ta’aziyyar rasuwar mahaifin ta

Related Posts

Hukumar Shari’a da Hukumar Tace Finafinai za su haɗa gwiwa don tsaftace tarbiyya a Kano
Labarai

Hukumar Shari’a da Hukumar Tace Finafinai za su haɗa gwiwa don tsaftace tarbiyya a Kano

July 11, 2025
Labarai

Jarumin Kannywood, Baba Ƙarami ya yi magana kan ganin sa da aka yi kan keken guragu 

July 10, 2025
Tsohuwar jarumar Kannywood, Halisa tana neman addu’a
Labarai

Tsohuwar jarumar Kannywood, Halisa tana neman addu’a

July 9, 2025
Mawaƙin Manzon Allah, Abdullahi Ɗan Gano ya rasu
Labarai

Mawaƙin Manzon Allah, Abdullahi Ɗan Gano ya rasu

July 7, 2025
MOPPAN ta yi wa al’ummar Kano ta’aziyyar Aminu Ɗantata 
Labarai

MOPPAN ta yi wa al’ummar Kano ta’aziyyar Aminu Ɗantata 

June 29, 2025
Ƙungiyoyin harkar fim, KAFIGAN da MOPPAN, sun yi wa Rahama Sadau ta’aziyyar rasuwar mahaifin ta
Labarai

Ƙungiyoyin harkar fim, KAFIGAN da MOPPAN, sun yi wa Rahama Sadau ta’aziyyar rasuwar mahaifin ta

June 23, 2025
Next Post
Ƙungiyoyin harkar fim, KAFIGAN da MOPPAN, sun yi wa Rahama Sadau ta’aziyyar rasuwar mahaifin ta

Ƙungiyoyin harkar fim, KAFIGAN da MOPPAN, sun yi wa Rahama Sadau ta'aziyyar rasuwar mahaifin ta

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!