• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Wednesday, May 6, 2026
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Mahaifin Rahama Sadau mutumin kirki ne da son jama’a, inji Yerima Shettima

by ABBA MUHAMMAD
June 22, 2025
in Labarai
0
Mahaifin Rahama Sadau mutumin kirki ne da son jama’a, inji Yerima Shettima

Alhaji Yerima Shettima kusa da Rahama Sadau a lokacin da ake addu'a

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

Shugaban Ƙungiyar Tuntuɓa ta Matasan Arewa (AYCF) na ƙasa, Alhaji Yerima Usman Shettima, ya bayyana mahaifin Rahama Sadau a matsayin mutumin kirki, mai son jama’a.

Yerima, wanda shi ne mijin tsohuwar jarumar Kannywood Fati Ladan, ya yi wannan bayani ne a lokacin da ya je ta’aziyya gidan marigayin, wato marigayi Alhaji Ibrahim Sadau.

Shugaban ya shaida wa mujallar Fim cewa, “Haƙiƙa duk wanda ya san Alhaji Ibrahim Sadau, ya san cewa mutum ne mai kirki da son jama’a. Ko da na wannan wuri na ƙara tabbatar da haka.

“Babu abin da ya kamata mu yi masa a yanzu da ya wuce addu’ar neman gafara da rahama a gare shi.”

Ya ƙara da cewa, “Muna kuma fatan halayen sa na kirki su bi shi. Allah ya yafe masa kurakuran sa, Allah ya albarkaci dukkan zuri’ar sa.”

Shettima a yayin da suke addu’a tare da mahaifiyar su Rahama, wato Hajiya Bilkisu
Yerima a cikin ‘yan’uwan marigayi Alhaji Ibrahim Sadau suna addu’a

Yerima da tawagar sa sun isa gidan su Rahama da misalin ƙarfe 5:00 na yamma, inda kai-tsaye aka yi masu jagora zuwa inda Rahama take.

An gudanar da addu’o’in neman gafara ga mamacin, wadda Malam Ibrahim PDP ya jagoranta.

Haka kuma sun shiga cikin falon da Hajiya Bilkisu, wato mahaifiyar su Rahama take, sun yi mata ta’aziyya tare da yin addu’o’i.

Daga nan kuma suka fita waje inda ‘yan’uwan mamacin suke, nan ma suka yi masu gaisuwa da addu’a.

Rahama da ‘yan’uwan ta sun yi wa su Yerima godiya da fatan Allah ya maida su gida lafiya.

Loading

Tags: Alhaji Ibrahim SadauRahama Sadaurasuwar mahaifita'aziyyaYerima Shettima
Previous Post

Yadda mahaifin mu ya rasu kwana ɗaya bayan ya dawo daga Makkah – Abba, yayan Rahama Sadau

Next Post

Ƙungiyoyin harkar fim, KAFIGAN da MOPPAN, sun yi wa Rahama Sadau ta’aziyyar rasuwar mahaifin ta

Related Posts

Rasuwar dattijon Kannywood, Nura Shareef, ta girgiza ‘yan fim
Labarai

Rasuwar dattijon Kannywood, Nura Shareef, ta girgiza ‘yan fim

February 22, 2026
Daraktar fim ta ƙi karɓar awad saboda kisan gillar da Isra’ila take yi a Gaza
Labarai

Daraktar fim ta ƙi karɓar awad saboda kisan gillar da Isra’ila take yi a Gaza

February 21, 2026
Fitaccen furodusa Kunle Afolayan ya yi haɗin gwiwa da Jamhuriyar Benin kan shirya finafinai
Labarai

Fitaccen furodusa Kunle Afolayan ya yi haɗin gwiwa da Jamhuriyar Benin kan shirya finafinai

February 19, 2026
An naɗa Farfesa Tengya matsayin sabon shugaban Cibiyar Koyon Finafinai ta Ƙasa
Labarai

An naɗa Farfesa Tengya matsayin sabon shugaban Cibiyar Koyon Finafinai ta Ƙasa

February 15, 2026
Alƙali ya ci Samha Inuwa tara ko ta je kurkuku wata 6
Labarai

Alƙali ya ci Samha Inuwa tara ko ta je kurkuku wata 6

February 13, 2026
Hukumar EFCC ta kama jarumar Kannywood, Samha Inuwa, saboda goge majina da takardun naira
Labarai

Hukumar EFCC ta kama jarumar Kannywood, Samha Inuwa, saboda goge majina da takardun naira

February 3, 2026
Next Post
Ƙungiyoyin harkar fim, KAFIGAN da MOPPAN, sun yi wa Rahama Sadau ta’aziyyar rasuwar mahaifin ta

Ƙungiyoyin harkar fim, KAFIGAN da MOPPAN, sun yi wa Rahama Sadau ta'aziyyar rasuwar mahaifin ta

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!