• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Wednesday, May 6, 2026
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Mahaifin Rahama Sadau ya rasu kwana 1 bayan ya dawo daga aikin Hajji

by ABBA MUHAMMAD
June 22, 2025
in Labarai
0
Mahaifin Rahama Sadau ya rasu kwana 1 bayan ya dawo daga aikin Hajji

Marigayi Alhaji Ibrahim Sadau tare da 'ya'yan sa: Abba Sadau da ƙanwar sa, Rahama Sadau

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

ALLAHU Akbar! Da asubahin yau Lahadi, Allah ya ɗauki ran mahaifin shahararriyar jaruma, Rahama Sadau, a Kaduna.

Rahama da kan ta ta bayyana wannan abin baƙin cikin a soshiyal midiya.

Su ma ƙannen ta sun bayyana labarin rasuwar a intanet.

Mujallar Fim ta ruwaito cewa a jiya Asabar ne dattijon ya dawo daga aikin Hajji, kuma ya rasu ne a wani asibiti sakamakon gajeren rashin lafiya.

Za a yi jana’izar sa anjima da misalin ƙarfe 10:00 na safe a gidan sa da ke Unguwar Rimi, Kaduna.

Rahama Sadau da mahaifin ta, marigayi Alhaji Ibrahim Sadau

Alhaji Ibrahim Sadau ya rasu ya bar ‘ya’ya tara, amma shida aka fi sani saboda alaƙar su da industirin Kannywood, wato Abba da ƙannen sa Rahama, Zainab, A’isha, Fatima, sai kuma Baffa.

Ɗimbin ‘yan fim da sauran jama’a sun yi wa Rahama da ‘yan’uwan ta gaisuwa, suna addu’ar Allah ya jiƙan mahaifin nata.

Shugaban Hukumar Shirya Finafinai ta Nijeriya (NFC), Alhaji Ali Nuhu, ya yi ta’aziyya a soshiyal midiya, inda ya ce, “Inna lillahi wa inna ilaihir raji’un. Allah ya jiƙan shi da rahama, ya sa mutuwa hutu ne a gare shi. Allah ya ba wa iyalan shi da ‘yan’uwa haƙuri da juriyar rashin shi, amin.”

Ƙungiyar Kadawood da ke Kaduna ta miƙa ta’aziyyar ta ga Rahama Sadau.

Ƙungiyar, a ƙarƙashin jagorancin Malam Nura MC, ta ce, “A madadin dukkan membobin ƙungiyar Kadawood Film Makers, muna miƙa ta’aziyyar mu ta musamman ga Rahama Sadau da dukkan ‘yan’uwan ta, dangane da rasuwar mahaifin su.

“Haƙiƙa wannan babban rashi ne ba gare su kaɗai ba, har ma da al’umma baki ɗaya.

“Muna roƙon Allah maɗaukakin Sarki ya jiƙan mamacin, ya sa Aljanna ce makomar sa. Allah ya ba su haƙurin jure wannan babban rashin.”

Allah ya jiƙan Alhaji Ibrahim Sadau, amin.

Loading

Tags: Alhaji Ibrahim SadauKadawoodRahamaSadaurasuwar mahaifi
Previous Post

Kiran Gwamnatin Tarayya ga ‘yan jarida: Ku zama jigo wajen gina dimokiraɗiyyar Nijeriya

Next Post

Yadda mahaifin mu ya rasu kwana ɗaya bayan ya dawo daga Makkah – Abba, yayan Rahama Sadau

Related Posts

Rasuwar dattijon Kannywood, Nura Shareef, ta girgiza ‘yan fim
Labarai

Rasuwar dattijon Kannywood, Nura Shareef, ta girgiza ‘yan fim

February 22, 2026
Daraktar fim ta ƙi karɓar awad saboda kisan gillar da Isra’ila take yi a Gaza
Labarai

Daraktar fim ta ƙi karɓar awad saboda kisan gillar da Isra’ila take yi a Gaza

February 21, 2026
Fitaccen furodusa Kunle Afolayan ya yi haɗin gwiwa da Jamhuriyar Benin kan shirya finafinai
Labarai

Fitaccen furodusa Kunle Afolayan ya yi haɗin gwiwa da Jamhuriyar Benin kan shirya finafinai

February 19, 2026
An naɗa Farfesa Tengya matsayin sabon shugaban Cibiyar Koyon Finafinai ta Ƙasa
Labarai

An naɗa Farfesa Tengya matsayin sabon shugaban Cibiyar Koyon Finafinai ta Ƙasa

February 15, 2026
Alƙali ya ci Samha Inuwa tara ko ta je kurkuku wata 6
Labarai

Alƙali ya ci Samha Inuwa tara ko ta je kurkuku wata 6

February 13, 2026
Hukumar EFCC ta kama jarumar Kannywood, Samha Inuwa, saboda goge majina da takardun naira
Labarai

Hukumar EFCC ta kama jarumar Kannywood, Samha Inuwa, saboda goge majina da takardun naira

February 3, 2026
Next Post
Yadda mahaifin mu ya rasu kwana ɗaya bayan ya dawo daga Makkah – Abba, yayan Rahama Sadau

Yadda mahaifin mu ya rasu kwana ɗaya bayan ya dawo daga Makkah - Abba, yayan Rahama Sadau

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!