• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Tuesday, July 15, 2025
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Mahaifin Rahama Sadau ya rasu kwana 1 bayan ya dawo daga aikin Hajji

by ABBA MUHAMMAD
June 22, 2025
in Labarai
0
Mahaifin Rahama Sadau ya rasu kwana 1 bayan ya dawo daga aikin Hajji

Marigayi Alhaji Ibrahim Sadau tare da 'ya'yan sa: Abba Sadau da ƙanwar sa, Rahama Sadau

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

ALLAHU Akbar! Da asubahin yau Lahadi, Allah ya ɗauki ran mahaifin shahararriyar jaruma, Rahama Sadau, a Kaduna.

Rahama da kan ta ta bayyana wannan abin baƙin cikin a soshiyal midiya.

Su ma ƙannen ta sun bayyana labarin rasuwar a intanet.

Mujallar Fim ta ruwaito cewa a jiya Asabar ne dattijon ya dawo daga aikin Hajji, kuma ya rasu ne a wani asibiti sakamakon gajeren rashin lafiya.

Za a yi jana’izar sa anjima da misalin ƙarfe 10:00 na safe a gidan sa da ke Unguwar Rimi, Kaduna.

Rahama Sadau da mahaifin ta, marigayi Alhaji Ibrahim Sadau

Alhaji Ibrahim Sadau ya rasu ya bar ‘ya’ya tara, amma shida aka fi sani saboda alaƙar su da industirin Kannywood, wato Abba da ƙannen sa Rahama, Zainab, A’isha, Fatima, sai kuma Baffa.

Ɗimbin ‘yan fim da sauran jama’a sun yi wa Rahama da ‘yan’uwan ta gaisuwa, suna addu’ar Allah ya jiƙan mahaifin nata.

Shugaban Hukumar Shirya Finafinai ta Nijeriya (NFC), Alhaji Ali Nuhu, ya yi ta’aziyya a soshiyal midiya, inda ya ce, “Inna lillahi wa inna ilaihir raji’un. Allah ya jiƙan shi da rahama, ya sa mutuwa hutu ne a gare shi. Allah ya ba wa iyalan shi da ‘yan’uwa haƙuri da juriyar rashin shi, amin.”

Ƙungiyar Kadawood da ke Kaduna ta miƙa ta’aziyyar ta ga Rahama Sadau.

Ƙungiyar, a ƙarƙashin jagorancin Malam Nura MC, ta ce, “A madadin dukkan membobin ƙungiyar Kadawood Film Makers, muna miƙa ta’aziyyar mu ta musamman ga Rahama Sadau da dukkan ‘yan’uwan ta, dangane da rasuwar mahaifin su.

“Haƙiƙa wannan babban rashi ne ba gare su kaɗai ba, har ma da al’umma baki ɗaya.

“Muna roƙon Allah maɗaukakin Sarki ya jiƙan mamacin, ya sa Aljanna ce makomar sa. Allah ya ba su haƙurin jure wannan babban rashin.”

Allah ya jiƙan Alhaji Ibrahim Sadau, amin.

Loading

Tags: Alhaji Ibrahim SadauKadawoodRahamaSadaurasuwar mahaifi
Previous Post

Kiran Gwamnatin Tarayya ga ‘yan jarida: Ku zama jigo wajen gina dimokiraɗiyyar Nijeriya

Next Post

Yadda mahaifin mu ya rasu kwana ɗaya bayan ya dawo daga Makkah – Abba, yayan Rahama Sadau

Related Posts

Hukumar Shari’a da Hukumar Tace Finafinai za su haɗa gwiwa don tsaftace tarbiyya a Kano
Labarai

Hukumar Shari’a da Hukumar Tace Finafinai za su haɗa gwiwa don tsaftace tarbiyya a Kano

July 11, 2025
Labarai

Jarumin Kannywood, Baba Ƙarami ya yi magana kan ganin sa da aka yi kan keken guragu 

July 10, 2025
Tsohuwar jarumar Kannywood, Halisa tana neman addu’a
Labarai

Tsohuwar jarumar Kannywood, Halisa tana neman addu’a

July 9, 2025
Mawaƙin Manzon Allah, Abdullahi Ɗan Gano ya rasu
Labarai

Mawaƙin Manzon Allah, Abdullahi Ɗan Gano ya rasu

July 7, 2025
MOPPAN ta yi wa al’ummar Kano ta’aziyyar Aminu Ɗantata 
Labarai

MOPPAN ta yi wa al’ummar Kano ta’aziyyar Aminu Ɗantata 

June 29, 2025
Ƙungiyoyin harkar fim, KAFIGAN da MOPPAN, sun yi wa Rahama Sadau ta’aziyyar rasuwar mahaifin ta
Labarai

Ƙungiyoyin harkar fim, KAFIGAN da MOPPAN, sun yi wa Rahama Sadau ta’aziyyar rasuwar mahaifin ta

June 23, 2025
Next Post
Yadda mahaifin mu ya rasu kwana ɗaya bayan ya dawo daga Makkah – Abba, yayan Rahama Sadau

Yadda mahaifin mu ya rasu kwana ɗaya bayan ya dawo daga Makkah - Abba, yayan Rahama Sadau

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!