ƘUNGIYAR tsofaffin jaruman matan Kannywood masu aure (KAHOWA) ta karrama shahararren mawaƙi, Alhaji Dauda Adamu Abdullahi Kahutu (Rarara).
‘Ya’yan ƙungiyar sun karrama mawaƙin ne da wata garkuwa ta musamman a jiya Lahadi yayin ziyartar sa da su ka yi a gidan sa na Kano.
Shugabar ƙungiyar wadda ita ce ta jagoranci maziyartan, Hajiya Sakna Gadaz, ta bayyana cewa, “Dauda Kahutu Rarara ya na taimaka wa ƙungiyar sosai ‘financially’ don ganin kowace mace ta samu abin yi da za ta riƙe kan ta. A matsayi na na shugabar ƙungiyar, mun kai masa ziyara don nuna godiya da kuma ba shi ‘award’ don girmamawa. Allah ya saka da alkhairi, ya ƙara ɗaukaka.”

A lokacin ziyarar, Rarara ya ba ‘yan ƙungiyar shawara, inda ya ce, “Dukkan ku nan an san rawar da ku ka taka, yawanci waɗanda ba su kalle ku ba yanzu, ana ba su labarin ku, kun san abin da ku ka yi. Yanzu kun zama masu ba da shawarwari, kun zamar mana kamar madubi a wurin ‘yan baya. Shi ya sa na ke ƙoƙari in tambaya kowace matar aure ce? Saboda in ji daɗi in ce waɗannan matan aure ne, kuma su na zaune, kuma sun kafa wata ƙungiya wadda za ta ƙara jaddada wannan zaman auren nasu. A ɗan taƙaice kenan.”

Wata majiya ta shaida wa mujallar Fim cewa Rarara, wanda an san shi da taimakon jama’a, ya sha alwashin zai taimaka wa ƙungiyar.
Ya buƙace su da su yi ƙoƙari su yi wa ƙungiyar tasu rajista a hukumance.