• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Monday, June 30, 2025
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

An yi taron walimar saukar Alƙur’ani ta ‘yar Abba El-Mustapha

by DAGA MUKHTAR YAKUBU
October 23, 2023
in Labarai
1
Alhaji Abba El-Mustapha tare da A'isha da sauran iyalin sa a wajen taron

Alhaji Abba El-Mustapha tare da A'isha da sauran iyalin sa a wajen taron

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

A JIYA Lahadi, 22 ga Oktoba, 2023 aka yi taron walima na saukar karatun Alƙur’ani na ‘yar Shugaban Hukumar Tace Finafinai da Ɗab’i ta Jihar Kano, Alhaji Abba El-Mustapha, wato Aisha Abba El-Mustapha (Lateefa).

Taron ya gudana da yamma a gidan El-Mustapha da ke Titin Malam Aminu Kano, kusa da Ƙofar Gadon Ƙaya, a birnin Kano.

A wajen taron, wanda ‘yan’uwa da abokan arziki da dama su ka halarta, an yi karatun Alƙur’ani tare da addu’o’i, sannan kuma aka raba kyaututtuka ga yara. Ita ma amaryar saukar, wato Aisha, ta gabatar da karatu.

Aisha Abba El-Mustapha

Da ya ke jawabi dangane da taron, El-Mustapha ya ce ya shirya wannan taron ne domin ya nuna godiyar sa ga Allah da ya ba shi arzikin haihuwar ‘ya mai basira da ƙwazo, domin kuwa ta na shekaru 14 da haihuwa a duniya ta yi saukar Alƙur’ani, kuma sauka ba ta zuƙu ba, sauka ce ta hadda. 

Ya ce: “Ina godiya ga Allah da wannan arzikin da Allah ya yi mani, kuma zan kasance mai alfahari da wannan baiwa har ƙarshen rayuwa ta. 

“Allah mun gode maka, kuma muna ƙara godiya a gare ka da wannan baiwa.

“Kuma ina fatan duk waɗanda su ka zo wannan waje da ma waɗanda ba su samu damar zuwa ba Allah ya haɗa mu a ladar.”

‘Yan fim da dama sun halarci wajen, daga cikin su akwai Mustapha Ahmed (Alhaji Sheshe) da Bashir Abubakar Maishadda.

Alhaji Abba tare da ‘yar sa da ta yi saukar hadda, wato Aisha
A’isha na gabatar da karatun Alƙur’ani a wajen taron
Su Alhaji Sheshe da Maishadda tare da El-Mustapha da iyalin sa
Abba El-Mustapha tare da ‘yan’uwa da abokan arziki

Loading

Previous Post

Gasar ‘Ƙidaya Challenge’: Yadda ‘yan Arewa su ka juya wa mawaƙi Rarara baya

Next Post

Mahaifin marubuci Zubairu Balannaji ya kwanta dama

Related Posts

Ƙungiyoyin harkar fim, KAFIGAN da MOPPAN, sun yi wa Rahama Sadau ta’aziyyar rasuwar mahaifin ta
Labarai

Ƙungiyoyin harkar fim, KAFIGAN da MOPPAN, sun yi wa Rahama Sadau ta’aziyyar rasuwar mahaifin ta

June 23, 2025
Mahaifin Rahama Sadau mutumin kirki ne da son jama’a, inji Yerima Shettima
Labarai

Mahaifin Rahama Sadau mutumin kirki ne da son jama’a, inji Yerima Shettima

June 22, 2025
Yadda mahaifin mu ya rasu kwana ɗaya bayan ya dawo daga Makkah – Abba, yayan Rahama Sadau
Labarai

Yadda mahaifin mu ya rasu kwana ɗaya bayan ya dawo daga Makkah – Abba, yayan Rahama Sadau

June 22, 2025
Mahaifin Rahama Sadau ya rasu kwana 1 bayan ya dawo daga aikin Hajji
Labarai

Mahaifin Rahama Sadau ya rasu kwana 1 bayan ya dawo daga aikin Hajji

June 22, 2025
Masanin harshe, Korao Hamadou ya gabatar da haruffan rubutun Hausa na asali a taro a Kano
Labarai

Masanin harshe, Korao Hamadou ya gabatar da haruffan rubutun Hausa na asali a taro a Kano

June 20, 2025
Kotu a Kano ta tsare Tsulange, matashin da ke tare titi yana wanka da yin shigar banza
Labarai

Kotu a Kano ta tsare Tsulange, matashin da ke tare titi yana wanka da yin shigar banza

June 20, 2025
Next Post
Marigayi Alhaji Musa Balannaji da ɗan sa, Zubairu

Mahaifin marubuci Zubairu Balannaji ya kwanta dama

Comments 1

  1. Pingback: Walimar Saukar Alƙur’ani Na ‘Yar Abba El-Mustapha » HausaMini.Com.Ng

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!