• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Friday, July 4, 2025
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Sana’ar Kannywood ta saɓa wa Musulunci – mawaƙi Ibrahim Yala

by DAGA ALI KANO
November 16, 2023
in Labarai
0
Alhaji Ibrahim Sale Yala

Alhaji Ibrahim Sale Yala

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

HARKAR fim da ake yin ta yanzu a Kannywood ta yi hannun riga da koyarwar addinin Musulunci, a cewar mawaƙin siyasa mazaunin Kaduna, Alhaji Ibrahim Sale Yala.

Mawaƙin ya na magana ne kan hayaniyar da ta baibaye masana’antar a soshiyal midiya sakamakon kalamin da jarumi Abdalla Amdaz ya yi a gaban shugabannin Hukumar Hisbah ta Jihar Kano a cikin wannan makon, kalamin da wasu ‘yan fim ke ganin tozarci ne ga masana’antar.

Yala ya ce mutane sun ƙi karɓar gaskiya ne kan abin da Amdaz ya faɗa, kuma shi ɗin ma ya sha yin maganganu irin waɗannan a baya amma aka yi biris da shi.

A rubutun da ya yi a soshiyal midiya a yau, mawaƙin, wanda ya taɓa yin fice da wata waƙar Janar Muhammadu Buhari a shekarun baya, ya ce: “Mafi yawan musibu su na faruwa ne daga kangare wa ɗaukar wa’azi ko wasun ku su janyo muku. Ni Ibrahim Yala na sha yin maganganu irin na Amdaz ko ma waɗanda su ka fi nashi zafi domin a samu gyara a wannan masana’anta da Allah ya ƙaddara sai an gan mu a cikin ta.

“Wallahi thunma tallahi wannan harkar ta yi hannun riga da Allah tun tuni, sai dai idan ba za mu faɗi gaskiya ba saboda son rai ko jahilci na rashin sanin halal da haram.”

A nadamar da ya yi ta kasancewar sa ɗan Kannywood, mawaƙin ya ce ba ya sha’awar wani nasa ya shiga harkar fim ta hanyar sa ko kaɗan.

“Wallahi ni ba ma ɗan da na haifa ba ko wanda ban da alaƙa da shi – in dai sanadi na zai shiga fim – ba zan bari ba,” inji shi.

Ya ƙara da cewa, “Masana’antar da babu mai ganin girman wani saboda yawancin mu mun zubar da mutuncin junan mu. Babu albarka a abin da mu ke kira sana’a saboda mun kauce wa duk wani tsari na addini. Babu mai sawa ko hanawa a cikin masana’antar.”

Ga masu ganin laifin Amdaz kuwa, Yala ya ce: “Kun san gaskiya sai dai ku bi son rai, amma duk abin da aka faɗa ana aikatawa babu sharri ko son rai a ciki.”

Ya ce a kullum ya na nadamar zaman sa a Kannywood. “Wallahi ban taɓa tsintar kai na a harkar da kullum ta ke fita a rai na ba irin wannan harkar tamu,” inji shi.

Dangane da yadda wasu fitattun matan Kannywood su ke kece raini da dukiya kuwa, sai Yala ya ce: “Na taɓa magana da wani a kan yadda matan masana’antar da su ka yi suna su ke yi na rashin kamun kai da gadara gurin saɓa wa tsarin addini, sai ya ce, ‘Waɗannan yaran kusan su su ke riƙe da masana’antar domin ɗai ɗai wanda ba su bai wa kuɗi.’ Shi ya sa za ka ga yarinya ta yi ‘posting’ a bakin hotel bayan kwashe kwanaki ta na holewar ta, har ma ka ga ta rubuta, ‘Alhamdu lillah,’ sai ka ga kowa na tura mata ‘WOW, kin yi kyau!’ ko hoton alamar zuciya, ko wuta balbal.'”

Yala ya ƙara da cewa,”Ni da ku mun san sana’ar ta ba fim ba ne.

“Sannan haka wasu mazan cikin mu sun zama abokan hulɗar ‘yan siyasa waɗanda ba su da juriyar zama babu kuɗi, su miƙa kan su ko su zama kawalai ta kowacce irin siga.”

Mawaƙin ya ce a kan waɗannan zarge-zarge shi ganau ne ba jiyau ba, domin wani abin ma ya shafe shi kai-tsaye.

“Idan na ce zan ci gaba da rubuta abubuwan da na sani game da wannan masana’antar, gaskiya za a sha mamaki domin wasu abubuwan ma sun shafe ni kai-tsaye wallahi,” inji shi.

A ƙarshe ya yi addu’ar Allah ya “shiryar da mu hanya madaidaiciya, amin.”

Loading

Previous Post

Ɓatanci kan Kannywood: Furodusa Alhaji Sheshe zai maka jarumi Amdaz a kotu

Next Post

Kiran Tinubu ga editoci: Ku riƙa yaɗa kyawawan labarai don jawo zuba jari a Nijeriya

Related Posts

MOPPAN ta yi wa al’ummar Kano ta’aziyyar Aminu Ɗantata 
Labarai

MOPPAN ta yi wa al’ummar Kano ta’aziyyar Aminu Ɗantata 

June 29, 2025
Ƙungiyoyin harkar fim, KAFIGAN da MOPPAN, sun yi wa Rahama Sadau ta’aziyyar rasuwar mahaifin ta
Labarai

Ƙungiyoyin harkar fim, KAFIGAN da MOPPAN, sun yi wa Rahama Sadau ta’aziyyar rasuwar mahaifin ta

June 23, 2025
Mahaifin Rahama Sadau mutumin kirki ne da son jama’a, inji Yerima Shettima
Labarai

Mahaifin Rahama Sadau mutumin kirki ne da son jama’a, inji Yerima Shettima

June 22, 2025
Yadda mahaifin mu ya rasu kwana ɗaya bayan ya dawo daga Makkah – Abba, yayan Rahama Sadau
Labarai

Yadda mahaifin mu ya rasu kwana ɗaya bayan ya dawo daga Makkah – Abba, yayan Rahama Sadau

June 22, 2025
Mahaifin Rahama Sadau ya rasu kwana 1 bayan ya dawo daga aikin Hajji
Labarai

Mahaifin Rahama Sadau ya rasu kwana 1 bayan ya dawo daga aikin Hajji

June 22, 2025
Masanin harshe, Korao Hamadou ya gabatar da haruffan rubutun Hausa na asali a taro a Kano
Labarai

Masanin harshe, Korao Hamadou ya gabatar da haruffan rubutun Hausa na asali a taro a Kano

June 20, 2025
Next Post
Ministan Yaɗa Labarai Da Wayar Da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya na gabatar da jawabin Shugaba Tinubu a wajen Babban Taron Kungiyar Editocin Nijeriya (NGE)

Kiran Tinubu ga editoci: Ku riƙa yaɗa kyawawan labarai don jawo zuba jari a Nijeriya

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!