• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Sunday, June 8, 2025
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Ni ba fitinanniya ba ce, inji Adama matar Kamaye

by DAGA MUKHTAR YAKUBU
March 26, 2020
in Taurari
0
Hajiya Zahra'u Sani, Adama matar Kamaye

Hajiya Zahra'u Sani, Adama matar Kamaye

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram
FITACCIYAR ‘yar wasan talabijin ɗin nan na ‘Daɗin Kowa’ na tashar Arewa24, Hajiya Zahra’u Sani, wadda aka fi sani da Adama matar Kamaye, ta bayyana irin fitinar da ta ke yi wa mijin ta a cikin shirin da cewa ba halin ta ba ne na zahiri. Ta ce kawai dai labarin ne ya zo da haka, kuma a duk lokacin da jarumi ya ke son ya isar da saƙo ga al’umma, to sai ya yi abin da rol ɗin da ya hau ya zo da shi.
 
Zahra’u ta bayyana hakan ne a lokacin tattaunawar su da mujallar Fim dangane da rol ɗin nata.
 
Tun da farko sai da jarumar ta bayyana mana asalin ta da kuma yadda aka yi ta shigo harkar fim. 
 
Ta ce: “To ni dai Zahra’u Sani, wadda aka fi sani da Adama matar Kamaye a cikin shirin ‘Daɗin Kowa’, asali na ‘yar Gombe ce, a can aka haife ni, na tashi a can, na yi makaranta, sai kuma daga baya na dawo nan Kano na ci gaba da zama a wajen ‘yan’uwa na”.
 
Dangane da yadda ta samu shiga harkar fim kuwa, cewa ta yi, “Ina ganin kusan shekaru goma kenan da shigowa ta harkar fim, kuma na shigo ne ta sanadiyyar aminiya ta, wato Hajiya Zulai Bebeji, wadda ita ce na same ta na nuna mata sha’awa ta ta yin fim.
 
“Kuma a lokacin mu ka tafi; da man za ta je lokeshin, don haka ta tafi da ni, kuma mu na zuwa aka saka ni a fim wanda kuma shi ne fim ɗi na na farko, sunan sa ‘Kazar Tsafi’.
 
“Kuma tun daga lokacin na ci gaba da yin fim har zuwa yanzu.”
 
To yaya aka yi ta samu kan ta a cikin shirin ‘Daɗin Kowa’?
 
Zahra’u ta ce, “To gaskiya zan iya cewa al’amari ne daga Allah, domin an kira mutane ne za a tantance su, ni ma sai na je don na gwada sa’a ta,  kuma Allah ya sa na dace aka ɗauke ni a matsayin Adama.”
 
Da ya ke da fim ɗin kasuwa ta fara, mun tambaye ta bambancin fim ɗin kasuwa da fim mai dogon zango irin na talabijin.
 
Amsa: “To gaskiya ni a gani na tazara ce kamar tsakanin sama da ƙasa, domin kuwa shi wannan duniya ce ga baki ɗaya ta ke kallon ki, shi kuma na kasuwa sai wanda ya saya ya kai gidan sa, don haka fim ɗin ‘Daɗin Kowa’ ya fi karɓuwa a wajen mutane, domin na yi fim tsawon lokaci, amma ka ga mutane ba su san ni ba sai a ‘Daɗin Kowa’, don haka ‘Daɗin Kowa’ ne ya ɗaga ni duniya ta san ni.
 
“A baya ana ganin mu jifa-jifa a ce an san mu, amma kuma da mu ka shiga ‘Daɗin Kowa’ sai kowa ya san mu. 
 
“Yanzu za ka shiga taro sai ka na ɓuya, saboda idan mun shiga gari mu ka haɗu da yara, mu na fuskantar matsaloli, saboda ƙauna sai mutum ya ce wai sai ya taɓa jikin ka. To ka ga idan wannan ya taɓa wancan ya ce zai taɓa, sai su yaga maka kaya, ko kuma su cire maka gyale. 
 
“To wannan shi ya sa mu ke gudun yara wani lokacin, ko mu saka niƙab mu rufe fuskar mu in za mu fita.”
 
Zahra’u ta bayyana cewa irin gajiyar da ta ci da shirin ‘Daɗin Kowa’ “abin ba zai lissafu ba.” 
 
A cewar ta, “Har zuwa yanzu mu na cin gajiyar ne kuma za mu ci gaba da ci nan gaba. Don haka a wannan ɓangaren babu abin da zan ce sai dai godiya ga Allah.”
 
Daga ƙarshe, ta yi kira ga jama’a da su fahimci cewar yadda ta ke rayuwa a cikin ‘Daɗin Kowa’ ba haka rayuwar ta ta zahiri ta ke ba. “Domin wani lokacin na kan samu kai na wasu su tsare ni su rinƙa yi mini tambayar me ya sa na ke yi wa Kamaye abu kaza. To haka rol ɗin ya zo, don haka ba hali na ba ne.”

Loading

Previous Post

Buri na a ji amon tambari na a duk duniya, inji Zaliha ‘Yar Chamas

Next Post

Gidaje da mutane sun yi yawa a ‘Daɗin Kowa’, cewar Sallau

Related Posts

Na fi so in fito a matsayin masifaffiya a fim, inji Fa’iza Abdullahi
Taurari

Na fi so in fito a matsayin masifaffiya a fim, inji Fa’iza Abdullahi

December 25, 2024
Fim ɗi na mai suna ‘Baban Ladi’ na ja sosai, inji sabon furodusa Razaki jarumin ‘Daɗin Kowa’
Taurari

Fim ɗi na mai suna ‘Baban Ladi’ na ja sosai, inji sabon furodusa Razaki jarumin ‘Daɗin Kowa’

November 25, 2023
Sayyada Raihan Imam Ahmad (Ƙamshi)
Taurari

Fim riga ce ta arziki – Raihan Imam Ƙamshi

November 20, 2023
Saratu Abubakar
Taurari

Yadda ɗaukaka ta sa na ke rufe fuska – Saratu Abubakar

October 1, 2023
Safna Lawan
Taurari

Buri na a Kannywood ya kusa cika, inji Safna Lawan

August 24, 2023
Cewar Fanan Buzuwa: "Ba zan iya auren ɗan fim ba"
Taurari

‘Yan fim kada mu riƙe sana’a ɗaya – Fanan Buzuwa

June 11, 2023
Next Post
Umar Sani Jigirya ya ce Sallau daban, Umar daban

Gidaje da mutane sun yi yawa a 'Daɗin Kowa', cewar Sallau

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!