ALLAHU Akbar! Allah ya yi wa tsohon Kantoman Kano, Dakta Muhammadu Uba Adamu, rasuwa.
Dattijon ɗan shekara 85 ya rasu ne ɗazu gab da shan ruwa a Asibitin Nassarawa, a Kano.
Dakta Muhammadu dai shi ne mahaifin fitaccen malamin jami’a ɗin nan kuma manazarcin adabin Hausa, Farfesa Abdalla Uba Adamu, wanda kuma shi ne mataimakin shugaba (Vice-Chancellor) na Buɗaɗɗiyar Jami’ar Nijeriya (National Open University of Nigeria, NOUN).
Shi ma marigayin, ya taɓa koyarwa a ‘School of Management’ da ke Kano. Kafin nan ya taɓa riƙe muƙamin Kantoman Kano.
Bayan haka, marubucin littattafan tarihi ne da kuma waƙoƙin gyara tarbiyya.
Littattafan sa sun haɗa da ‘Sabon Tarihin Asalin Hausawa’, sannan kuma Aminu Ala ya rera waƙoƙin sa da su ka fito a faifai mai suna ‘Duniya Makaranta’.
Dakta Muhammadu Adamu ya bar mata biyu da ‘ya’ya 17 da jikoki masu yawa.
Ana sa ran gobe da safe za a yi jana’izar sa a Kano.
Ya zuwa yanzu har ɗimbin mutane sun aika wa da Farfesa Abdalla da sauran dangin sa saƙwannin ta’aziyya ta hanyar waya ko ta hanyar soshiyal midiya.