• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Friday, July 4, 2025
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Allah ya yi wa mahaifin furodusa Habibu Barde rasuwa

by DAGA MUKHTAR YAKUBU
April 26, 2023
in Labarai
0
Marigayi Alhaji Barde Muhammad

Marigayi Alhaji Barde Muhammad

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

A RANAR Talata, 25 ga Afrilu, 2023 Allah ya yi wa babban malamin addinin Muslunci da ke garin Azare, Jihar Bauchi, Malam Barde Muhammad, rasuwa. Shi ne mahaifin babban furodusan Kannywood Alhaji Habibu Barde Muhammad.

Marigayin, mai shekaru 96 a duniya, ya rasu ne bayan ya sha fama da rashin lafiya in inda aka kwantar da shi a babban asibitin Federal Medical Centre da ke Azare na tsawon lokaci kafin a sallame shi ya koma gida in da kuma daga baya Allah ya yi masa cikawa a  gidan sa.

Malam Barde fitaccen malami ne wanda ya shafe tsawon rayuwar sa ya na koyar da Ƙur’ani da sauran littattafan Muslunci.

Ɗan sa, Alhaji Habibu, shi ne furodusan fim ɗin ‘Nihla’ kuma Mataimakin Shugaban ƙungiyar MOPPAN na yankin arewa-ta-tsakiya. Shi ne na uku a cikin ‘ya’yan sa guda 34.

Tuni dai Shugaban MOPPAN na ƙasa, Dakta Ahmad Sarari, ya aika da saƙon ta’aziyyar sa kamar yadda Kakakin kungiyar Al-Amin Ciroma ya wallafa.

Ciroma ya ce a takardar ta’aziyya da Sarari ya aika wa Habibu Barde, ya bayyana rashin a matsayin babbar jarrabawa ce, kuma ya yi addu’ar Allah ya gafarta masa, ya sa Aljanna ce makomar sa, sannan ya kyautata bayan sa.

Ita ma Majalisar Ƙoli ta Dattawan Kannywood, ta hannun Sakataren ta Malam Kabiru Muhammad Maikaba ta bayyana ta’aziyyar ta tare da alhini. Ƙungiyar ta ce: “Wannan majalisa na taya ɗan’uwa Alhaji Habibu Barde Muhammad da sauran ‘yan’uwa jimamin wannan babban rashin da aka yi. Mu na taya ka tare da sauran ‘yan’uwa addu’ar Allah ya jiƙan Baba, Allah ya yafe masa kurakuran sa, ya sa Aljanna ce makoma. A madadin masana’antar Kannywood, wannan majalisa na tare da ku wajen yi wa Baba addu’a Allah ya kula da abin da ya bari. Ku kuma Allah ya ba da ladar haƙuri.”

Loading

Previous Post

Furodusa Abubakar Anka na so a farfaɗo da zumunci irin na da a tsakanin ‘yan Kannywood

Next Post

Na ji rasuwar Balaraba Tanko kamar mutuwar mata ta, inji Ashiru Bazanga ‘Sawun Keke’

Related Posts

MOPPAN ta yi wa al’ummar Kano ta’aziyyar Aminu Ɗantata 
Labarai

MOPPAN ta yi wa al’ummar Kano ta’aziyyar Aminu Ɗantata 

June 29, 2025
Ƙungiyoyin harkar fim, KAFIGAN da MOPPAN, sun yi wa Rahama Sadau ta’aziyyar rasuwar mahaifin ta
Labarai

Ƙungiyoyin harkar fim, KAFIGAN da MOPPAN, sun yi wa Rahama Sadau ta’aziyyar rasuwar mahaifin ta

June 23, 2025
Mahaifin Rahama Sadau mutumin kirki ne da son jama’a, inji Yerima Shettima
Labarai

Mahaifin Rahama Sadau mutumin kirki ne da son jama’a, inji Yerima Shettima

June 22, 2025
Yadda mahaifin mu ya rasu kwana ɗaya bayan ya dawo daga Makkah – Abba, yayan Rahama Sadau
Labarai

Yadda mahaifin mu ya rasu kwana ɗaya bayan ya dawo daga Makkah – Abba, yayan Rahama Sadau

June 22, 2025
Mahaifin Rahama Sadau ya rasu kwana 1 bayan ya dawo daga aikin Hajji
Labarai

Mahaifin Rahama Sadau ya rasu kwana 1 bayan ya dawo daga aikin Hajji

June 22, 2025
Masanin harshe, Korao Hamadou ya gabatar da haruffan rubutun Hausa na asali a taro a Kano
Labarai

Masanin harshe, Korao Hamadou ya gabatar da haruffan rubutun Hausa na asali a taro a Kano

June 20, 2025
Next Post
Marigayiya Hajiya Balaraba Tanko (Sa'adatu Abubakar)

Na ji rasuwar Balaraba Tanko kamar mutuwar mata ta, inji Ashiru Bazanga 'Sawun Keke'

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!