• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Monday, May 18, 2026
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

An fara rukunin ‘C’ na shirin N-Power tare da matakan da matasa za su bi

by DAGA WAKILIN MU
March 12, 2021
in Nijeriya
1
An fara rukunin ‘C’ na shirin N-Power tare da matakan da matasa za su bi
0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

GWAMNATIN Tarayya ta kawo ƙarshen dogon jiran da ake yi na fara aiwatar da rukuni na uku (Batch C) na shirin N-Power wanda za a shigar cikin jerin shirye-shiryen rage matsin rayuwa, wato ‘National Social Investment Programmes’ (NSIPs).


Mai bada shawara kan aikin jarida ga Ministar Harkokin Jinƙai, Agaji da Inganta Rayuwa, Madam Nneka Ikem, ita ce ta bayyana haka a ranar Alhamis cikin wani saƙo da ta tura a Twitter. 


A cewar ta, ana kira ga dukkan waɗanda su ka cike takardun nema shiga shirin da su ci gaba da sauraren bayanai kan tantancewar su. 


Ta rubuta cewa: “Labari da ɗumi-ɗumi! Za a ƙaddamar da @npower_ng rukuni na C a yau a manhajar @NSIP_NG wato NASIMS.

 
“Masu neman shiga #BatchC su ci gaba da duban fitowar bayanai kan tantancewar su. @nairaland @NigerianYouthC2 @Npower_Reps”. 

Idan an tuna, kimanin matasan Nijeriya miliyan biyar ne su ka rubuta takardar neman shiga shirin N-Power a cikin 2020. Rajistar shiga kashin farko na shirin an fara ta ne a ranar 26 ga Yuni, 2020, kuma manufar shirin shi ne a sama wa matasa 500,000 aikin yi.


 A cewar minista Sadiya Umar Farouq, ana so ne a sama wa matasa damarmaki da za su ƙware ta yadda za a iya ɗaukar su aiki ta hanyar ba su dabarun yin sana’a.


Tun ba a je da nisa ba, a yau ne ma’aikatar ta bada sanarwar cewa duk wanda ya cike buƙatar shirin na N-Power ya shiga mataki na gaba na rukunin ‘C’ kamar yadda aka ce za a sanar. 


Saboda haka a sanarwar da Babban Sakataren ma’aikatar, Alhaji Bashir Nura Alkali, ya bayar a yau, ma’aikatar ta yi kira ga dukkan waɗanda su ka nemi shiga cikin rukunin da su gaggauta bin waɗannan matakan ba tare da ɓata lokaci ba:

1. Su duba imel ɗin su da su ka bayar lokacin neman shiga shirin domin ganin matakan da za su bi su shiga gidan yanar shirin.


2. Su shiga www.nasims.gov.ng domin shiga gidan yanar masu neman a ɗauke su a shirin saboda su bada ƙarin bayanan da ake nema game da su.


3. Su bi umarnin da aka jera a gidan yanar tare da yin jarabawar intanet da aka tsara a wajen.

Previous Post

Iyan-Tama: Har yanzu da ni ake damawa a Kannywood

Next Post

Na sha gamuwa da masu sha’awa ta – Nafisa Salisu, jarumar ‘Macen Sirri’

Related Posts

Yadda CBN ke tallabe da tattalin arzikin Nijeriya, yayin sa farashin ɗanyen mai ke faɗuwar-‘yan-bori a kasuwa
Nijeriya

Yadda CBN ke tallabe da tattalin arzikin Nijeriya, yayin sa farashin ɗanyen mai ke faɗuwar-‘yan-bori a kasuwa

November 7, 2025
Shirin ƙarfafa jari: CBN ya shawarci bankuna marasa ƙarfi su haɗe ko su rage wa lasisin su geji
Nijeriya

Shirin ƙarfafa jari: CBN ya shawarci bankuna marasa ƙarfi su haɗe ko su rage wa lasisin su geji

November 2, 2025
Bankin CBN ya yunƙuro: Naira ta hana dala numfashi mai ƙarfi a ƙarshen Oktoba
Nijeriya

Bankin CBN ya yunƙuro: Naira ta hana dala numfashi mai ƙarfi a ƙarshen Oktoba

November 2, 2025
Bankin CBN ya ƙaryata ƙazafin sayar wa manyan dillalan mai dala biliyan 1.259 domin su shigo da fetur daga waje
Nijeriya

Bankin CBN ya ƙaryata ƙazafin sayar wa manyan dillalan mai dala biliyan 1.259 domin su shigo da fetur daga waje

October 29, 2025
Tinubu ya yi adalci ga dukkan yankunan Nijeriya – Ministan Yaɗa Labarai
Nijeriya

Tinubu ya yi adalci ga dukkan yankunan Nijeriya – Ministan Yaɗa Labarai

August 31, 2025
Nijeriya

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar da Sababbin Cibiyoyin Maganin Ciwon Daji

July 24, 2025
Next Post
Na sha gamuwa da masu sha’awa ta – Nafisa Salisu, jarumar ‘Macen Sirri’

Na sha gamuwa da masu sha’awa ta - Nafisa Salisu, jarumar 'Macen Sirri'

Comments 1

  1. Usman shuaibu says:
    5 years ago

    Usmanshuaibuadamu19@yahoo.com

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!