FITACCEN direban nan wanda Alhaji Mamman Shata ya waƙe, Alhaji Umaru Ɗan Ɗanduna, ya samu tallafin kayan abinci da kuɗin cefane daga wani bawan Allah.
Hakan ya biyo bayan wata hira da aka yi da ɗan jarida kuma marubuci Ibrahim Sheme a gidan Rediyon Tarayyar Nijeriya na Kaduna kan fitacciyar waƙar nan ta Shata mai taken “Umaru Ɗan Ɗanduna Na Gwandu”, inda a ƙarshen hirar ya bayyana halin rashin lafiya da tsohon direban ya ke ciki.
To, sai wani bawan Allah wanda ya na ɗaya daga cikin dattawan Arewa ya tausaya wa Alh. Umaru Ɗan Ɗanduna bayan ya saurari hirar, kuma ya bada agajin kuɗi N100,000 gare shi ta ta hanyar Sheme.
Nan da nan Sheme ya tura marubuci kuma ɗan jarida Maje El-Hajeej Hotoro ya sanar da Alh. Umaru taimakon da aka yi masa, da sunan wanda ya bayar da kuɗin.
Alh. Umaru ya yi murna ƙwarai da gaske tare da godiya ga wannan bawan Allah, wanda ba ya so a bayyana sunan sa.
Bisa shawara da Alh. Umaru da iyalin sa, sai Sheme da Maje su ka kasa wannan kuɗi gida biyu – tare da amincewar wanda ya bada kuɗin – su ka kashe N50,000 wajen saya wa Alh. Umaru kayan abinci domin akwai buƙatar su.
A ranar Juma’a, 17 ga Janairu, 2019 aka kai kayan tallafin da kuma kuɗin inda aka miƙa su a gare shi a gidan sa da ke unguwar Gwanar Jaba a cikin garin Kano.
Wakilin mujallar Fim, wanda tare da shi Maje ya sawo kayan aka kai, ya ruwaito cewa kayan sun haɗa da buhun shinkafa, taliya, makaroni, man girki, sabulun wanka da na wanki, da sauran su.
Haka kuma an ba Alh. Umaru tsabar sauran kuɗin hannu da hannu.
A lokacin da ya ke karɓar agajin, tsohon direban ya ƙara yin godiya ga Allah dangane da wannan gudunmawa da aka ba shi, sannan ya ƙara gode wa mutumin da ya yi masa agajin.
Daga ƙarshe, Alhaji Umaru ya gode wa duk waɗanda su ka yi ɗawainiya don ganin saƙon ya isa gare shi.

A nasa ɓangaren, shi ma Ibrahim Sheme ya ce: “Ina addu’ar Allah ya saka wa wannan bawan Allah da alheri, kuma ya ba Alh. Umaru Ɗan Ɗanduna lafiya da nisan kwana, amin.
“Haka kuma ina addu’ar Allah ya jiƙan Alh. Mamman Shata, wanda a bayyane ta ke cewa duk da yake ya bar duniya amma har yanzu mutane su na cin arzikin sa ta hanyoyi daban-daban.”