WATA tsohuwar jaruma a Kannywood, Amina Abubakar, ta bayyana cewa yanzu masana’antar finafinan Hausa waje ne maras tsafta.
Jarumar ta faɗi haka ne a lokacin wata zantawa da ta yi da mujallar Fim inda ta kwatanta harkar fim a yau da yadda ake yin ta a da.
Ita dai Amina, ta shafe kusan shekara 25 ta na harkar fim. Ta fara tun ana wasan daɓe, zuwa dirama a gidan talbijin na CTV Kano, zuwa fim ɗin bidiyo har zuwa shirin ‘Kwana Casa’in’ na gidan talbijin na Arewa24.
A tattaunawar ta wakilin mu a Kano dangane da halin da harkar fim ta samu kan ta a ciki a yanzu, Amina ta ce, “A lokacin baya harkar akwai taimakon juna da ganin girman na gaba, ta yadda ko furodusa ko darakta idan akwai wanda ya ke gaba da shi to ya na girmama shi ne, ba zai kalli kan sa a matsayin darakta ba.
“Kuma duk lokacin da mu ka fita aiki za ka ga wajen zaman maza daban, na mata daban; kuma idan mace ta je da lulluɓi to har a gama aikin ta na tare da abin ta.
“Sannan babu maganar bambanci wajen abinci, duk haɗuwa ake yi a abinci iri ɗaya, wani lokacin ma matan da su ke wajen su ne za su dafa abincin.
“Amma yanzu abubuwa duk sun canza, babu wani mai girmama wani sai dai idan kai ake yayi sai a zo ana girmama ka, ana kamun ƙafa da kai.”
Jarumar ta ƙara da cewa, “Sam wannan ɗabi’ar babu ita a lokacin da aka kafa harkar fim. Daga baya ne aka shigo da ita.
“Wannan ya sa a yanzu rigingimu su ka yi yawa a masana’antar, aka kasa magance su, saboda babu mai ganin girman wani, kowa da inda ya sa gaba.”
Daga ƙarshe, Amina ta yi kira ga ‘yan fim da su dawo da kyawawan ɗabi’un da aka san harkar fim da su tun farkon kafuwar ta, domin wannan shi ne zai sa a samu ci-gaban da ake buƙata a masana’antar gaba ɗaya.
![]()






