KAMAR kowane sashe na jama’a, su ma ‘yan fim ɗin Hausa su na aure tare da hayayyafa. Mujallar Fim ce a kan gaba wajen bada labaran irin waɗannan abubuwa na farin ciki kamar yadda ake gani a shafin Ranar Murna. Kamar kowace shekara, a bana ma mun kawo maku jerin labaran aurarraki da haihuwa da aka yi waɗanda su ka danganci ‘yan fim da mawaƙan da ke cikin Kannywood. Ga su kamar haka:
AURE
Asabar, 30 ga Janairu:Mawaƙi Umar Ɗanhausa da Fatima Bashir, a masallacin Juma’a na Ɗanfodiyo da ke Unguwar Sanusi, Kaduna, a kan sadaki N50,000.
Asabar, 30 ga Janairu:Furodusa Abba Sadau da Zainab Musa Yarima, a masallacin A’ishatu Ɗan’iyan Misau da ke Titin Shagari, unguwar Badarawa, Kaduna, a kan sadaki N100,000.


Juma’a, 5 ga Fabrairu:Fitaccen jarumi Rabi’u Rikadawa ya aurar da ‘yar sa Fatima ga jarumi Salisu Abdullahi (Babangida), a masallacin Kabala Junction da ke Titin Nnamdi Azikiwe (Bypass), Kaduna, a bisa sadaki N100,000.

Juma’a, 12 ga Fabrairu:Tsohuwar jaruma Fati KK ta koma gidan tsohon mijin ta Alhaji Mu’azu Yusuf. An ɗaura auren a gidan su da ke Sabon Kawo, Kaduna.
Juma’a, 12 ga Fabrairu:An ɗaura auren Editan jaridar Rariya kuma jarumi a Kannywood, Aliyu Ahmad, da sahibar sa, Hauwa Sa’idu Gambo, a masallacin Juma’a na Babbar Kasuwar Muhammadu Buhari da ke garin Karu, yankin Abuja, a kan sadaki N100,000.


Juma’a, 26 ga Fabrairu:Darakta Sheikh Isah Alolo da Basira Isma’il, a wani masallacin Juma’a da ke Titin Galadimawa, unguwar Hayin Ɗanmani, Kaduna, a kan sadaki N100,000.
Asabar, 27 ga Fabrairu:Mawaƙi Ibrahim Saleh (Yala) da Halima Muhammad Kauru (Sima), a Masallacin Sarkin Musulmi Bello da Unguwar Sarki, Kaduna, a bisa sadaki N100,000.
Asabar, 27 ga Fabrairu:Mawaƙi Mas’ud Idris da A’isha Abubakar, a wani Masallaci da ke Bakin Boda, Unguwar shanu, Kaduna, a kan sadaki N70,000.

Asabar, 27 ga Maris:Mawaƙi kuma jarumi Abdu Boda da Hafsat Sabi’u Sani, a gidan Muntari Masko da ke Layin Zana a unguwar Ƙofar Marusa, Katsina, a kan sadaki N50,000.
Asabar, 27 ga Maris:Fitacciyar jaruma Hafsat Idris ta aurar da ‘yar ta Khadija Kabir ga Abubakar Ibrahim Muhammad, a unguwar Ɗandago cikin ƙwaryar Kano, a kan sadaki N50,000.
Juma’a, 4 ga Yuni:Editan riƙo na mujallar Fim, Abba Muhammad, da Jamila Ibrahim Dassi, a Masallacin Sheikh Ja’afar Mahmud Adam da ke Unguwar Dosa, Kaduna, a bisa sadaki N70,000.
Juma’a, 18 ga Yuni:Tsohuwar fitacciyar jaruma Naja’atu Muhammad da fitaccen ɗan ƙwallon ƙafa Abdullahi Shehu, a Masallacin Umar Bin Khattab da ke Titin Zariya, Kano, a kan sadaki N50,000.
Asabar, 7 ga Agusta:Fitacciyar jaruma Zahra Muhammad (Diamond Zahra) ta yi aure a asirce.

Juma’a, 20 ga Agusta:Fitaccen jarumi kuma mawaƙi Garzali Miko da Habiba Umar Ahmad Dikwa (Yarinya) a Masallacin Fajrul Islam da ke unguwar Rigasa, a kan sadaki N200,000.
25 ga Agusta:Fitacciyar mawaƙiya Maryam A. Baba (Sangandale) da matashin mawaƙi Abdul Kafinol sun cika shekara biyu da aure. Maryam ta wallafa hotunan da su ka ɗauka domin nuna murnar su a Instagram.
Asabar, 25 ga Satumba:Fitaccen furodusa kuma jarumi Abdullahi Abbas (Ubangari) da Zulaihat Ishaq Abdulrasheed, a Masallacin Adarawa, Jantiti, Rigasa, Kaduna, a bisa sadaki N200,000.
Laraba, 6 ga Oktoba:Fitaccen darakta kuma jarumi Al-Amin Ciroma da fitacciyar jaruma Wasila Isma’il sun wallafa hotuna kwafe bakwai a Instagram don murnar cikar su shekara 19 da aure.
Juma’a, 26 ga Nuwamba:Fitacciyar jaruma Maryam Musa Waziri da tsohon ƙan ƙwallon ƙafa Tijjani Babangida, a Kaltungo, Jihar Bauchi.


Lahadi, 12 ga Disamba:Fitaccen mawaƙi Abdul D. One da Ummu-Salma (Salma Fresh), a Layin Transfomer, Kwanar ‘Yan Ghana da ke unguwar Tudun Murtala, Kano, a kan sadaki N100,000.
20 ga Disamba:Tsohuwar fitacciyar jaruma Fati Ladan da mijin ta Yerima Shettima sun cika shekara takwas da aure. Sun yaɗa hotunan murna. Daga bisani, Fati ta yi hirar musamman da mujallar Fim inda ta shawarci matan Nijeriya kan sirrin zama mai ɗorewa da mazajen auren su.
Juma’a, 24 ga Disamba:Fitaccen futodusa, marubuci kuma ɗan jarida Alhaji Ibrahim Sheme, ya aurar da ‘yar sa, Malama A’isha, ga sahibin ta, Malam Abubakar Muhammad Bello, a Masallacin Malam Khamis Al-Misri, da ke Titin Nnamdi Azikiwe, Western Bypass, kusa da Titin Dutsin-ma, Kaduna, a kan sadaki N100,000.

HAIHUWA
Talata, 3 ga Agusta:Allah ya albakaci mawaƙi Sagir Ɗanyaro (Baban Kausar) da matar sa Fatima Muhammad da tagwaye duk mata. Fatima ta haihu a Asibitin Kadpoly, Kaduna. An raɗa wa jariran Hassana da Hussaina, amma mahaifiyar su na kiran su da Amna da Amra.
10 ga Agusta:Fitacciyar jaruma Jamila Umar Nagudu ta yi murnar zagayowar ranar haihuwar ta. Jamila, wadda uwa ce ga ɗan ta ɗaya, wato Mus’ab, ba ta shirya wani biki a bayyane ba, amma ta ɗora hotunan musamman da ta ɗauka domin wannan rana a Instagram.

26 ga Satumba:Allah ya albarkaci fitaccen jarumi Mustapha Musty da matar sa Ghadir Mahmud Shareef da samun ɗan fari. Ghadir, wadda ake wa laƙabi da Soha, ta haifi santalelen yaro a birnin Kano.
Juma’a, 10 ga Oktoba:Fitaccen mawaƙi Nura M. Inuwa da matar sa Amina sun samu ƙaruwa da ɗiya mace a Kano. An raɗa jaririyar suna Amina (Mifra).
21 ga Oktoba:Fitacciyar jaruma Amal Umar ta cika shekara 23 da haihuwa. Don nuna murnar wannan rana, Amal ta wallafa hotunan ta da ta ɗauka a situdiyo a Instagram.

Asabar, 6 ga Nuwamba: Allah ya azurta fittacen jarumi Adam A. Zango da Safiyya Umar Chalawa da ‘ya mace, a asibiti a Kaduna. An raɗa wa jarinya suna Furaira (Diana), sunan mahaifiyar Adam A. Zango.
![]()






