AN ɗaura auren matashiyar jarumar nan da ke Kaduna, Hauwa’u Abubakar (Fulani), wadda aka fi sani da Hauwa Rafin Guza, a jiya Asabar, 29 ga Janairu, 2022.
An ɗaura auren Hauwa da sahibin ta Muhammad Lawal Habeeb (Bala) da misalin ƙarfe 2:00 na rana a ƙofar gidan iyayen ta da ke lamba K12, Titin Fulani da ke unguwar Rafin Guza, Kaduna, kan sadaki N100,000.


Kafin ranar ɗaurin auren, a ranar Juma’a aka yi bikin Ranar Fulani a gidan su jarumar.

Sai dai kuma duk da gayyatar da jarumar ta yi wa abokan sana’ar ta, ba su yi mata kara ba domin kuwa daga matan har mazan babu wanda ya halarta sai ubagidan ta, darakta Abdullahi Abu Uku, sai wani mawaƙi mai suna Salim.
Allah ya ba su zaman lafiya da zuri’a ɗayyiba, amin.
ALiyu
Muhammad
Muhammad alhassan
Mashaallah Allah yasanya alheri
Allah sa mutu ka raba aminn