BABBAN mai taimaka wa fitaccen mawaƙi Alh. Dauda Adamu Abdullahi Kahutu (Rarara) a ɓangaren soshiyal midiya, Malam Rabi’u Garba Gaya, ya bayyana cewa maigidan nasa ba zai karɓi matasan nan guda biyu da su ka kama hanya daga Kaduna zuwa Kano a ƙafa domin ziyarar Rarara ɗin ba.
Su dai waɗannan, Mustapha Iliyasu da Anas Lawal, an ruwaito a soshiyal midiya cewa magoya bayan jam’iyyar APC ne kuma ‘yan ga-ni-kashe-nin ɗan takarar shugabancin ƙasa Asiwaju Bola Ahmed Tinubu.
Jaridar Rariya ce ta ba da labarin su a Facebook, inda ta ce matasan sun shaida mata cewa sun shirya tafiyar ne musamman domin ganawa da Rarara, kuma su ƙara masa ƙwarin gwiwa a bisa irin gudunmawar da ya ke bai wa APC da Tinubu.
Haka kuma sun ce akwai kyauta ta musamman da su ka tanada domin bai wa mawaƙin idan sun haɗu.
A halin yanzu dai matasan sun ba Jihar Kaduna baya, su ka nausa zuwa Kano.

Sai dai kuma da mujallar Fim ta tuntuɓi Rabi’u Garba Gaya domin sanin ko Rarara ya san da wannan tattaki da matasan su ke yi domin sa, sai ya amsa da cewa, “Mu ma yadda ka ga labarin a soshiyal midiya, haka mu ma mu ka gan shi.
“Kuma magana ta gaskiya, ko sun zo ba na tsammanin za a karɓe su, duba da yadda matasa yanzu sun ɗauki wannan abu a matsayin sana’a. Gaskiya dalilin kenan.
“Sannan kuma wataƙila lokacin da za su iso garin ma ba ya nan, tunda har yanzu ba ya nan. To ka ji inda kes ɗin ya ke.
“Amma dai zan yi maganar da shi; duk abin da ya ce sai in sanar da kai.”