BBC Hausa sun bayyana cewa a gobe ne za su fara gabatar da wani shiri a kan mata da samari mai suna ‘Mahangar Zamani’ wanda za a riƙa nunawa a YouTube.
A sanarwar da BBC Hausa su ka turo wa mujallar Fim, sun bayyana cewa ma’aikan gidan yaɗa labaran ne za su riƙa haɗa sabon shirin, kuma su wallafa shi a YouTube.
Sanarwar ta ƙara da cewa burin su shi ne matasa da mata su kalli shirin.
Sanarwar ta ce shirin na tsawon minti 25 za a riƙa haska shi sau biyu a mako kuma zai riƙa taɓo al’amuran yau da kullum waɗanda matasa ke magana a kan su.
Wadda za ta riƙa gabatar da shirin dai ita ce Madina Maishanu, kuma wannan shiri na musamman zai riƙa taɓo al’amuran da ake tattaunawa waɗanda za a riƙa wallafawa a kafafen sada zumunta da kuma kafafen yaɗa labarai irin na da.

Madina ‘yar jarida ce wadda ta ƙware a kafofin yaɗa labarai iri daban-daban, kuma ta na cikin rukunin masu aiki a fagen soshiyal midiya. Ta taka rawa wajen jawo hankalin masu saurare da kallo matasa da mata a kafafen sada zumunta na zamani na BBC Hausa.
Ita ce ta riƙa kawo labarin nan na zanga-zangar da aka yi kan George Floyd kai-tsaye daga gaban fadar White House.
A tsokacin da ta yi kan shirin, Madina ta ce, “Naɗa ni mai gabatar da ‘Mahangar Zamani’ da aka yi wani cikar buri ne a gare ni. Ina jin daɗin ganin cewa shirin zai kawo mu kan gaba kuma ya ba mu damar samun magance matsaloli.”
Sanarwar ta ce za a bada sanarwar adireshin da mutum zai bi ya shiga wajen shirin a shafukan YouTube da Facebook na BBC Hausa don masu kallo su shiga a duk lokacin da su ka ga dama.
Editan Sashen Hausa na BBC, Aliyu Tanko, ya ce: “Manufar shirin ita ce ta ba matasa da mata wata murya da kuma damar faɗin matsayin su a cikin al’ummar wannan zamani. Mu na so mu ba masu sauraren mu da kallon mu wata sabuwar fahimta da kuma damar ‘yancin yin muhawara a kan muhimman al’amura.”
Kashi na 1 – Dangantakar malamai da ɗalibai a jami’o’i: Kashi na farko na shirin ya dubi hulɗar da ba ta dace ba tsakanin malamai da ɗalibai a jami’o’in Nijeriya. A dukkan tsawon tattaunawar, masu kallo za su ga ra’ayoyi mabambanta a kan wannan zazzafan maudu’in.
Kashi na 2 – ‘Yancin mata a Arewacin Nijeriya: Wannan kashin zai yi warwarar ma’anoni daban-daban da mutane ke ba kalmar ‘yancin mata (feminism) daga yadda addini ya ƙarfafa mata, da yadda maza ke raina ƙarfin mata zuwa dankwafar da maza tare da cin fuskar su. A wannan kashin za ku ji ra’ayoyi daga wani namiji da wata mace.
Za a wallafa ‘Mahangar Zamani’ daga ƙarfe 10 na safe a ranar 2 ga Oktoba sannan daga nan za a riƙa yi sau biyu a mako.
Ku bi tattaunawar ta amfani da #MahangarZamani.
Mai neman ƙarin bayani sai ya tuntuɓi wannan imel ɗin: marina.forsythe@bbc.co.uk