• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Wednesday, August 26, 2026
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Buhari ya rantsar da Yakubu a matsayin Shugaban INEC a karo na biyu

by DAGA WAKILIN MU
December 9, 2020
in Nijeriya
0
Farfesa Mahmood Yakubu lokacin da ake rantsar da shi

Farfesa Mahmood Yakubu lokacin da ake rantsar da shi

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram
SHUGABAN Ƙasa Muhammadu Buhari a yau Laraba ya rantsar da Farfesa Mahmood Yakubu a matsayin Shugaban Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC ), a wa’adi na biyu don gudanar da aiki na tsawon shekara biyar.
 
Kamfanin Dillancin Labarai na Nijeriya (NAN) ya ruwaito cewar an yi taron rantsarwar ne a jim kaɗan kafin a fara taron mako-mako na Majalisar Zartaswa ta Tarayya ta hanyar intanet a Fadar Shugaban Ƙasa da ke Abuja.
 
Idan kun tuna, tun a ranar 1 ga Disamba ne Majalisar Dattawa ta amince da sake naɗin Yakubu a matsayin Shugaban na INEC.
 
Tabbatar da naɗin na Yakubu da majalisar ta yi ya biyo bayan rahoton da Kwamitin ta kan INEC, wanda Sanata Kabiru Gaya ke shugabanta, ya gabatar a lokacin zaman ta.
 
A ranar 25 ga Nuwamba ne Shugaba Buhari ya aika da sunan Yakubu ga Majalisar Dattawan domin ta amince da naɗin sa a karo na biyu.
 
Buhari ya sake naɗa Yakubu ne a matsayin Shugaban INEC don gudanar da aikin shekara biyar a ranar 27 ga Oktoba.
 
Yakubu dai shi ne mutum na farko da zai jagoranci hukumar a karo biyu.
 
A jawabin da ya yi ga manema labarai da ke Fadar Shugaban Ƙasa bayan an rantsar da shi, Yakubu ya sha alwashin zai ƙara zage dantse wajen tabbatar da an riƙa gudanar da zaɓuɓɓuka fisabilillahi a ƙasar nan.
 
Ya nanata cewa INEC za ta ci gaba da haɗa gwiwa da Majalisar Tarayya wajen tabbatar da an yi wa dokokin zaɓe garambawul a cikin lokaci.
 
Ya ce: “A bayyane yake cewa mun nuna a zaɓuɓɓukan da aka yi cikin ‘yan watannin nan cewa ana samun cigaba wajen shirya zaɓuɓɓuka kuma za su ci gaba da inganta kamar yadda ya kamata.
 
“Majalisar Tarayya za ta shirya taron faɗin albarkacin bakin ‘yan ƙasa a kan yi wa dokokin zaɓe garambawul.
 
“Wannan ya na da muhimmanci kuma a wannan karon, tare da haɗin gwiwar Majalisar Tarayya, za mu tabbatar da cewa an zartar da ƙudirin garambawul ɗin a cikin hanzari, kuma da zaran an yi hakan, zai taimaka mana ƙwarai da gaske wajen tunƙarar dukkan ƙalubalen da ke gaban mu.
 
“An riga an yi nisa wajen shirye-shiryen zaɓuɓɓukan shekara ta 2023; mu na buƙatar tabbaci saboda haka hurumin dokokin zaɓe na da muhimmanci, wanda idan babu shi ba za mu iya fito da namu ƙa’idojin da dokokin ba.
 
“Idan babu namu ƙa’idojin da dokokin, ba za mu iya kammala aiki kan kundin horas da ma’aikatan wucin-gadi da za su yi aiki a lokutan zaɓuɓɓukan ba.
 
“Saboda haka daga nan, zan tafi kai-tsaye zuwa Majalisar Tarayya ne, saboda a fara aiki gadan-gadan, wanda mun riga mun fara shi.’’
 
NAN sun fahimci cewa taron na Majalisar Zartaswa ta Tarayya da aka yi ta hanyar intanet ya samu halartar Mataimakin Shugaban Ƙasa Yemi Osinbajo, da Sakataren Gwamnatin Tarayya, Boss Mustapha, da Shugaban Ma’aikatan Ofishin Shugaban Ƙasa, Farfesa Ibrahim Gambari, da Mai Bada Shawara Kan Harkokin Tsaro (NSA), Manjo-Janar Babagana Monguno (ritaya).
 
Sauran ‘yan majalisar da su ka halarci taron ido da ido sun haɗa da Antoni Janar kuma Ministan Shari’a, Abubakar Malami, da Ministan Yaɗa Labarai Da Al’adu, Alhaji Lai Mohammed, da Ministan Ayyuka Da Gidaje, Babatunde Fashola, da Ministan Harkokin Jiragen Sama, Sanata Hadi Sirika, da Ministar Harkokin Mata, Pauline Tallen, da Ministar Harkokin Jinƙai, Agaji Da Inganta Rayuwa, Sadiya Umar Farouk, da sauran su.
 
 
 
 

Loading

Previous Post

Aminu Ala ya zama Ɗanburam Sarkin Gobir

Next Post

Gwamnatin Kano ta sha alwashin za ta kare martabar harshen Hausa

Related Posts

Yadda CBN ke tallabe da tattalin arzikin Nijeriya, yayin sa farashin ɗanyen mai ke faɗuwar-‘yan-bori a kasuwa
Nijeriya

Yadda CBN ke tallabe da tattalin arzikin Nijeriya, yayin sa farashin ɗanyen mai ke faɗuwar-‘yan-bori a kasuwa

November 7, 2025
Shirin ƙarfafa jari: CBN ya shawarci bankuna marasa ƙarfi su haɗe ko su rage wa lasisin su geji
Nijeriya

Shirin ƙarfafa jari: CBN ya shawarci bankuna marasa ƙarfi su haɗe ko su rage wa lasisin su geji

November 2, 2025
Bankin CBN ya yunƙuro: Naira ta hana dala numfashi mai ƙarfi a ƙarshen Oktoba
Nijeriya

Bankin CBN ya yunƙuro: Naira ta hana dala numfashi mai ƙarfi a ƙarshen Oktoba

November 2, 2025
Bankin CBN ya ƙaryata ƙazafin sayar wa manyan dillalan mai dala biliyan 1.259 domin su shigo da fetur daga waje
Nijeriya

Bankin CBN ya ƙaryata ƙazafin sayar wa manyan dillalan mai dala biliyan 1.259 domin su shigo da fetur daga waje

October 29, 2025
Tinubu ya yi adalci ga dukkan yankunan Nijeriya – Ministan Yaɗa Labarai
Nijeriya

Tinubu ya yi adalci ga dukkan yankunan Nijeriya – Ministan Yaɗa Labarai

August 31, 2025
Nijeriya

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar da Sababbin Cibiyoyin Maganin Ciwon Daji

July 24, 2025
Next Post
Nura M. Inuwa ya na karɓar kyautar karramawa daga hannun Dakta Gawuna

Gwamnatin Kano ta sha alwashin za ta kare martabar harshen Hausa

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!