SHUGABAN Hukumar Tace Finafinai ta Jihar Kano, Alhaji Isma’il Na’abba (Afakallah), ya ce ya yafe wa wani matashi ɗan fim mai suna Aliyu Sabo Bakin-Zuwo wanda ya zazzage shi a wani guruf na WhatsApp.
Wannan ya biyo bayan gafarar sa da ya nema.
Shi dai Aliyu, ya shiga guruf mai suna ‘Kannywood Vanguard’ ne ya tarar ana sukar Afakallah kan dokar nan da ya kafa ta hana yin fim a kan kidinafin ko ƙwacen waya. Ba tare da ya bi zaren tattaunawar ba sai ya rubuta muggan kalamai a kan shugaban.
Amma a wani bidiyo da ya yi, Aliyu ya nemi afuwar Afakallah kan abin da ya yi.
Ya ce ya yi kalaman ne bisa kuskuren fahimta kuma hakan ba zai ƙara faruwa ba.
Da ya ke bada lamarin yadda abin ya faru, Aliyu ya ce, “Akwai wani guruf wanda mu ke amfani da shi na ‘Kannywood Vanguard’, da ya haɗa jarumai, masu bada umarni da masu shirya fim, a cikin wannan group a Whatsapp, kasan cewar akwai masu ra’ayi daban-daban da su kan kawo maganganu na suka, musamman ga shi Afakallahu ɗin. To da yawa yawancin mutune saboda maganganu su na da yawa ba ka da damar da za ka ce sai ka je ka jiwo tun daga rajin magana wajen ɗari biyu ce, to sai na yi kuskure na fara da tsar daga inda bai kamata na ji ba sai na ji kamar an zo da ra’ayin shi Afakallahu na ba ya ƙaunar masa’antar ne.
“Amma cikin ikon Allah, bayan na fahimce shi ba daidai ba, sai na yi zage-zage na ɓatancin kalamai a kan sa.
”Ana haka kuma sai na yi wa kai na adalci cewa in koma baya mana in ji me ma Afakallahu ya yi har ake masa wannan kalaman a gidan. Sai na je na saurari bayanan da ya yi a wata hira da ya yi da gidan talabijin na TVC, sai na ji ashe shi Afakallahu ƙokari ya ke ya kare mutuncin al’adar mu ta Hausa da kuma harka ta tsaro ɗin nan da ta lalace ya ke ƙoƙarin cewar bai kamata a dinga nuna wa mutane yanda ake kidinafin ake satar waya ba wanda ma bai san ana yi ba in ya kalli irin wannan fim ɗin sai ya zo ya koya ya ce au, haka ma ake yi? Kamar misali an yi wani fim, ‘Gwaska’, yara duk ba su san ya ake a shiga makaranta a fasa a mammanna takardu dalilin wannan fim sai aka samu yara su na fasa abu su mammanna abu a bango sai su rubuta daga ‘Gwaska’ ne.”
Aliyu ya nemi afuwar masoyan sa bisa kalaman da ya yi kan Afakallah.
Lokacin da mujallar Fim ta ji ta bakin Afakallah kan wannan lamari a yau, shugaban hukumar ya ce, “Na haƙura kamar yadda ya bada haƙuri”.
“Ba za mu bari don Allah ya yi wa wani ni’ima ba kawai mutane su zauna su na zagin mu.
“Kuma wannan haƙuri da ya bayar, mun karɓa kuma mun yarda da cewa hakan ya zama horo a gare shi da kuma izna ga duk wanda ya ke so ya yi, da sauran su.”
Sai dai Afakallah ya nuna cewa mahassada ne su ka taso shi gaba, amma daga yanzu ba zai lamunta da haka ba.
Ya ce, “Ta ya za a yi don Allah ya ba wa mutum ni’ma ko ya ba shi shugabanci kawai mutane su ɗauki wannan abin ya zama abu ne da kawai na za su ci mutuncin mutum ya tafi kawai? Ba zai yiwu ba!”
Afakallah ya gargaɗi duk wani mai niyyar aikata irin wannan da cewa, “Duk wanda ya ke tunanin yin haka nan gaba ya shirya wa haka.”