• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Thursday, June 5, 2025
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Cewar Tinubu: Gwamnati na za ta mutunta ‘yancin kafafen yaɗa labarai, za ta karɓi yabo, gyara da suka daga ‘yan jarida da marubuta

* Ya gana da Ƙungiyar Mawallafa Jaridun Nijeriya

by WAKILIN MU
December 19, 2023
in Nijeriya
0
Cewar Tinubu: Gwamnati na za ta mutunta ‘yancin kafafen yaɗa labarai, za ta karɓi yabo, gyara da suka daga ‘yan jarida da marubuta
0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

SHUGABA Bola Tinubu ya ƙara jaddada cewa gwamnatin sa a ko yaushe za ta mutunta ‘yancin kafafen yaɗa labarai da ‘yan jarida, kuma za ta yi maraba hannu biyu da ra’ayoyin masu nuni da yin gyara, suka ko yabon gwamnatin sa.

Cikin sanarwar da Kakakin Yaɗa Labaran Shugaban Ƙasa, Ajuri Ngelale ya fitar, ya ce
Tinubu ya yi wannan bayani ranar Litinin, lokacin da ya gana da mambobin Ƙungiyar Mawallafa Jaridu ta Nijeriya (NPAN).

Shugaba Tinubu ya tabbatar masu da cewa zai zauna a tsanake ya duba buƙatar da suka bijiro masa da ita, wato ta neman a sassauta tsarin hada-hadar takardar buga jarida, wanda ke ci wa gidajen jaridu tuwo a ƙwarya ta hanyar tsadar takardun a cikin gida.

Da ya koma kan wahalhalun da matafiya ke fuskanta a yanzu lokacin tafiya hutun Kirsimeti da sabuwar shekara, Shugaba Tinubu ya ce gwamnatin tarayya za ta ɗauki matakan sauƙaƙa tsadar zirga-zirga da sufurin jiragen sama, na ƙasa da kuma kan titinan motoci.

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris ne ya jagoranci tawagar masu gidajen jaridun a wannan ziyarar da suka kai wa Shugaba Tinubu.

Shugaban ya ci gaba da cewa ana nan ana ɗaukar matakan da za a rage farashin gas.

“Na damu sosai dangane da abin da ke faruwa a cikin ƙasar nan. Ina gode maku kan goyon bayan da ku ke bayarwa da ra’ayoyi da sukar da ake yi wa gwamnatin mu. Ba domin goyon bayan wasu daga cikin ku ba, ba zan zama shugaban ƙasa ba, har ga ni a yanzu tare da ku a matsayin shugaba.

“Kun jajirce kan aikin ku cikin rintsi da tsanani. Don haka mu kuma za mu ci gaba da mutunta ra’ayoyin ku, ko da kuwa ba mu yarda da abin da ku ka faɗa kan mu ba.

“Abu ɗaya da zan faɗa maku shi ne, ina karanta kowace jarida, ina kuma karanta ra’ayoyin da ake rubutawa, har ma da shafukan manazarta da marubuta ra’ayoyi daban-daban,” inji Tinubu.

A jawabin sa, Ministan Yaɗa da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya jaddada kyakkyawar aniyar Gwamnatin Tarayya ta shata wa kafafen yaɗa labarai kyakkyawar shimfiɗa a ƙasar nan.

“Dimokraɗiyyar mu ta ginu ne a kan tsari da tafarkin ƙa’ida da tabbatar da komai bisa kyakkyawan tsarin doka da kuma ‘yancin yaɗa labarai da bayanai.

“Rawar da kafafen yaɗa labarai musamman jaridu ke bayarwa ta na da tasiri da muhimmanci a wannan turbar dimokraɗiyya,” cewar Minista Idris.

Daga nan Idris ya jinjina wa jagororin NPAN saboda samar da ƙungiya mai ƙarfin tattauna batutuwan da suka shafi ƙasa da kuma bayar da damar sauraren muryoyin jama’a mabambanta ra’ayoyi da fahimta.

Shi kuma Shugaban NPAN, kuma shugaban kamfanin Media Trust, masu buga Daily Trust, Trust TV da Aminiya, Malam Kabiru Yusuf, ya fara da yi wa Shugaba Tinubu murnar nasarar zaɓe da kuma nasara a Kotun Ƙoli. Daga nan ya ci gaba da lissafo matsalolin da suka dabaibaye masana’antu da hada-hadar takardar buga jaridu.

Loading

Tags: Bola TinubuKabiru Yusufmawallafan jariduMohammed IdrisNPAN
Previous Post

Jarumin Kannywood Shu’aibu Lilisco da Zulaihat sun samu Halima, sun cika shekara 20 da aure

Next Post

Tsohuwar jarumar Kannywood Fati Ladan da mijin ta sun yi walimar cikar su shekara 10 da aure

Related Posts

Tinubu ya tura wakilai zuwa Neja kan ambaliyar Mokwa da ta halaka sama da mutum 150
Nijeriya

Tinubu ya tura wakilai zuwa Neja kan ambaliyar Mokwa da ta halaka sama da mutum 150

May 31, 2025
Gwamnatin Nijeriya ta goyi bayan amfani da Ƙirƙirarrar Basira cikin ɗa’a a aikin jarida – Idris
Nijeriya

Gwamnatin Tarayya ta yi ta’aziyyar mutanen da suka rasu a ambaliyar garin Mokwa

May 30, 2025
Babu wasu masu juya Tinubu ta bayan fage – Idris
Nijeriya

Babu wasu masu juya Tinubu ta bayan fage – Idris

May 25, 2025
Shirye-shiryen Shugaba Tinubu Suna Buɗe Hanyar Farfaɗowar Tattalin Arzikin Nijeriya – Idris
Nijeriya

Shirye-shiryen Shugaba Tinubu Suna Buɗe Hanyar Farfaɗowar Tattalin Arzikin Nijeriya – Idris

May 20, 2025
Idris ya ƙaryata ji-ta-ji-tar an mayar da taron bayanin ministoci zuwa London
Nijeriya

Idris ya ƙaryata ji-ta-ji-tar an mayar da taron bayanin ministoci zuwa London

May 16, 2025
Tinubu ya yaba wa Sule Lamiɗo a taron ƙaddamar da littafin tarihin rayuwar sa
Nijeriya

Tinubu ya yaba wa Sule Lamiɗo a taron ƙaddamar da littafin tarihin rayuwar sa

May 13, 2025
Next Post
Tsohuwar jarumar Kannywood Fati Ladan da mijin ta sun yi walimar cikar su shekara 10 da aure

Tsohuwar jarumar Kannywood Fati Ladan da mijin ta sun yi walimar cikar su shekara 10 da aure

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!