EDITAN Riƙo na mujallar Fim, Malam Abba Muhammad, ya bayyana cewa ɗaya daga cikin burikan sa a rayuwa ya cika tunda Allah ya ba shi ‘ya mace, wadda ya raɗa wa suna Khadija.
Abba ya yi waɗannan kalamai ne a yau Juma’a a wurin taron bikin sunan ‘yar sa.
Matar sa, Jamila Ibrahim Dassi, ta haihu a ranar Juma’a, 5 ga Agusta, 2022, da misalin ƙarfe 10:50 na safe a wani asibitin kuɗi mai suna Vicas Specialist Hospital da ke Unguwar Sarki, Kaduna.
An raɗa wa jaririyar suna Khadija (Fanan) a yau Juma’a, 12 ga Agusta, 2022, a masallacin Umar Bin Khattab da ke Ghana Close, Malali, Kaduna. Babban limamin masallacin, Malam Musa Umar Alkanawi, shi ne ya jagoranci addu’ar raɗin sunan.
Haka kuma an yi taron suna a gidan mahaifiyar Abba da ke Sardauna Crescent, Kaduna.

Da ya ke zantawa da mujallar Fim, Abba ya nuna farin cikin sa game da samun wannan ƙaruwa da ya yi, ya ce, “Na yi matuƙar murna da samun ‘ya mace, domin tun kafin na yi aure na ke addu’ar Allah ya ba ni ‘ya mace a farko idan Allah ya nufe ni da yin auren.
“Alhamdu lillah ɗaya daga cikin burika na ya cika ta wannan ɓangaren, tunda na raɗa wa ‘ya ta suna Khadija.”

A kan dalilin da ya sa ya ke son wannan suna, har ka raɗa wa ‘yar sa haka, ɗan jaridar ya ce, “Lallai wannan suna ya na da matuƙar muhimmaci a gare ni da ma sauran ‘yan’uwa na. Sunan yayar mahaifiya ta ne, ta na da matuƙar muhimmanci a rayuwar mu. Tsawon shekaru Allah bai ba ta haihuwa ba, amma ta riƙe mu tamkar ita ta haife mu. Wannan dalili ya sa na ga ya zama wajibi a gare idan Allah ya azurta ni da ‘ya mace in raɗa mata sunan ta.”
Allah ya raya Khadija, ya kuma albarkaci rayuwar ta, amin.

