HAƊAƊƊIYAR Ƙungiyar Masu Shirya Finafinai ta Nijeriya (MOPPAN) ta bayyana cewa ta na goyon bayan ƙarar da babban furodusa Hamisu Lamiɗo Iyan-Tama ya kai wani mutum mai ɓata sunan ‘yan fim a Facebook.
Mujallar ta ruwaito a jiya cewa Iyan-Tama ta maka wani matashi mai suna Imam Aliyu Indabawa a Babbar Kotun Jihar Kano saboda cin zarafin sa da ya yi a wani rubutu da ya yi a Facebook tare da yun jama’u kan dukkan ‘yan Kannywood.
Kotu ta miƙa wa Indabawa da sammaci a jiya Litinin inda ta buƙace shi da ya bayyana a kotu don amsa zargin cin zarafi da ɓata suna.
A yayin da ya ke yin tsokacin uwar ƙungiyar ‘yan fim kan al’amarin, kakakin MOPPAN na ƙasa, Malam Al-Amin Ciroma, ya faɗa wa mujallar Fim cewa, “Ɗaukar mataki a kan irin waɗannan mutane ɗaiɗaiku da kuma duk wata ƙungiya da ke cin mutunci da ɓatanci ga ‘yan fim a kan abin da ba su ji ba ba su gani ba shi ne abu mafi fifiko da mu ka sa a gaba.”
Ciroma, wanda darakta ne kuma jarumi, ya ƙara da cewa: “Misali, kowace ƙungiya da ta shigar da ƙara, MOPPAN za ta mara masu baya don ganin lallai an ƙwato masu haƙƙin su, haka nan kuma a ɗaiɗaikun su. Duk wanda ya yi irin wannan mu na goyon bayan sa don shi ne adalci.
“Ta ɗaya ɓangaren kuma, idan akwai wanda ya ke da matsala da wani ɗan fim, idan matsalar ta kai ba zai iya zuwa ga ƙungiya ya kawo ƙara ba, to ya kai ga hukuma, ya daina ɗaukar doka a hannun sa.
“A ɓangare na biyu kuma, masu shaci-faɗi, irin su su na nan da yawa, wanda babu abin da su ke so illa su samu ‘followers’ ko kuma su burge wasu mutanen da su ke so su burge. Waɗannan idan su na yi a da, to yanzu za su san cewa kan mu a haɗe ya ke, sai mun ƙwato wa kowa haƙƙin sa daidai gwargwado.
“Mu ba hukuma ba ne, amma a ƙungiyance mu na da kyakkyawar alaƙa da dukkan hukumomi, kuma su na mara mana baya a kan dukkan wanda ya nemi ya ci zarafin ɗan fim ko ita masana’antar ko kuma kowacce daga cikin ƙungiyoyin ‘yan fim.
“To wannan shi ne ra’ayin mu a kan dukkan mai neman ɓatanci ga ‘yan fim.”
Sai dai Ciroma bai fito ya bayyana irin mara wa Iyan-Tama bayan da za su yi ba.
Wata majiya ta shaida wa mujallar Fim cewa tun a watannin baya Iyan-Tama ya sanar da Shugaban MOPPAN na ƙasa, Dakta Ahmad Sarari, da shugaban ƙungiyar ‘yan fim ta Jihar Kano, Malam Ado Ahmad Gidan Dabino, da Majalisar Dattawan Kannywood wannan matsalar ta ɓatanci da Indabawa ya ke aikatawa, to amma babu wani hoɓɓasa da su ka yi a kai.
Ko a yau Talata sai da marubucin Facebook ɗin ya sake wallafa rubutun da ya fara jawo fitinar, wanda ya yi tun a bara, sannan ya maimaita maganar da ya faɗa a baya, ya ce, “Ina ƙara faɗa: mafi yawan ‘yan fim ba mutanen kirki ba ne kuma su na lalata tarbiyya. Duk wanda zai ƙyale mutanen kirki ya hidimta wa ‘yan fim shi ma ba mutumin kirki ba ne ko waye.”