• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Thursday, July 31, 2025
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Daɗi 2: Ɗandugaji ya cika shekara 50, kuma ya zama shugaban ICT a MAKIA

by DAGA MUHAMMAD LAWAN RANO
April 24, 2021
in Labarai
0
Daɗi 2: Ɗandugaji ya cika shekara 50, kuma ya zama shugaban ICT a MAKIA
0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

ABUBUWA biyu masu daɗi sun faru ga fitaccen jarumi Tukur S. Tukur (Ɗandugaji) kwanan nan: na farko ya cika shekara 50 da haihuwa, na biyu kuma an tabbatar masa da muƙamin shugaban sashen kula da kafafen sadarwa (ICT) na babban filin jirgin sama na Malam Aminu (MAKIA) da ke Kano.

Kafin wannan tabatarwar, jarumin ya kwashe shekara ɗaya da watanni a matsayin muƙaddashin shugaban sashen.

Hukumar kula da filayen jirage ta Nijeriya (FAAN) ta tabbatar masa da muƙamin a ranar 13 ga Maris, 2021.

Ɗandugaji na ɗaya daga cikin sanannun jarumai a ɓangaren barkwanci a Kannywood, kuma jigajigai wajen assasa wannan masana’anta. 

A hirar sa da mujallar Fim, jarumin ya kuma bayyana cewa yanzu haka ya dawo harkar fim gadan-gadan.

Ɗandugaji, wanda ya gode wa Allah da ya ba shi damar cika shekara 50 a duniya, ya faɗi abin da wasu su ka ce da aka ba shi wannan muƙami.

Ya ce, “Gaskiya na tsorata matuƙa bisa wannan nauyin da aka ɗora min a matsayin wanda zai jagoranci wani sashe da ke filin jirgi, to amma duk da cewa mutane da dama sun sha faɗin cewa ya za a yi a ɗauki ɗan fim ɗin barkwanci a ba shi wannan muƙamin, su na ganin kamar ba zan iya ba, sai kuma ga shi Allah ya yi dole ni zan jagoranci wurin.

Tukur S. Tukur (Ɗandugaji) a bakin aiki

“Kamar yadda na samu takardar tabbatarwa daga hukumar kula da filayen jirgi ta Nijeriya, wanda a cikin ta su ka tabbatar mani da hakan, bayan na shafe kusan shekaru 18 ina aiki tun ina a matsayin mai aikin wucin-gadi, wato ‘casual’ a turance, daga baya kuma na zama cikakken ma’aikaci, na kuma samu goyon baya na ga soyayya da fatan alkairi daga cikin ma’aikata da ‘yan’uwa da abokanan arziki wanda da man idan lokaci irin wannan ya zo dole sai ka gamu da ƙalubale in dai a kan shugabanci ne.”

Ɗan wasan ya ƙara da cewa, “Shi wannan ƙarin girma da na samu ya zo ne a daidai lokacin da saura wata ɗaya da kwana biyar in cika shekara hamsin cif cif a duniya a ranar 18 ga Afrilu, 2021. An haife ni a 1971, ka ga shekara hamsin, to mai shekaru irin wannan a zamanin nan ba wasa ba ne don duk mutumin da aka ce ya shekara hamsin a duniya ya zama dattijo babu kuma wani mulki da ba zai iya riƙewa ba, babu kuma wata magana da ba zai iya shanyewa ba.

“Saboda haka wannan mulki ya zo min a shekarun dattijontaka, duk da cewar jiki na da yanayi na bai wuce ka kalle ni ka ce min ban wuce shekaru irin 35 ba zuwa 40 saboda yanayin irin ƙirar da Ubangiji ya yi mani, to amma dai shekarun su na da yawa; shekara 50 ba wasa ba ne; duk wani cikar hankali a yanzu ta zo wa mutum kuma duk wata martabawa da za a yi wa mutum don shekarun sa ba a min ba don  shekaru na sun kai.

“Yanzu ba abin da zan iya cewa sai dai fatan nasara da gamawa lafiya domin yanzu ni na zama matashin dattijo. Ga yara a ƙarƙashi na, ga kuma iyalai da dama da na ke kula da su.”

A game da harkar fim kuma, tsohon jarumin ya ce, “Ni da man ban daina fitowa a finafinai ba kamar yadda a kwanakin baya na gaya wa wannan mujallar, domin kuwa ba zan ce na daina fim ba sai dai ni akwai yadda na ɗauki fim wanda ba sai na maimaita ba. Idan Allah ya sa an kirawo ni ina zaune, zan je na yi fim.

“Kuma da man ai tsarawa za a yi matuƙar bai taɓa yanayin aiki na ba, idan kuma ya taɓa yanayin aiki na ba zan bar aiki na in zo in yi fim ba. Duk wanda za mu yi harkar fim zan gaya masa yanayin lokutan da na ke da su, idan ya ga zai iya to, in kuma ba zai iya ba ka ga dai na gaya masa lokuta na sun fi zuwa ranar ƙarshen mako duk da ita ma ɗin wani lokacin mu na aiki amma zan san yadda zan yi na zo na yi wa wanda ya gayyace ni aiki.”

Wani ƙarin albishir daga jarumin zuwa ga masoyan sa shi ne: “A watan Fabrairu da ya gabata na 2021 na samu gayyata har guri uku inda na yi finafinai guda uku masu dogon zango wanda ɗaya za a riƙa haska shi a gidan talbijin na Arewa24, ɗaya kuma a Tauraruwa TV, na ƙarshen shi har yanzu ba a sa inda za a haska shi ba. Kuma in Allah ya yarda mutane za su ga irin rawar ganin da na taka wanda ba sai na faɗa ba, su da kan su za su yi alƙalanci, kuma a nan ne za su gane cewa har yanzu Ɗandugaji ya na nan bai mutu ba a harkar fim.”

A ƙarshe, Ɗandugaji ya yi kira ga jama’a da su ci gaba da taya su da addu’a tare da yi musu fatan alkairi da kyautata zato a gare su da kuma a riƙe juna a matsayin ‘yan’uwa.

Ya ce babu shakka dole a rayuwa saɓa ni zai iya shiga tsakanin ka da wani, “sai mun zama masu yafiya da juna tunda wata rana duniyar nan yadda aka yi hirar nan da ni wata ran sai ka yi hira da wani nawa a kan mutuwa ta, ka ga kenan kowa zai mutu.

“Jan hankili na kawai mu zama masu yafiya, mu zama masu juriya da junan mu, mu kuma zama masu riƙe alƙawari.”

Loading

Tags: DandugajiICTKannywoodMAKIATukur S. Tukur
Previous Post

2023: INEC ta yi wa sassan ta na cikin gida garambuwal

Next Post

‘Sirrin Ɓoye’: Hatsabibiyar yarinya a Kannywood

Related Posts

Wani mai suna Bashir Abdullahi ya damfare ni miliyan bakwai da rabi, inji Halisa
Labarai

Wani mai suna Bashir Abdullahi ya damfare ni miliyan bakwai da rabi, inji Halisa

July 28, 2025
Gaskiyar magana kan ji-ta-ji-tar ‘mutuwar’ Aminu Ala
Labarai

Gaskiyar magana kan ji-ta-ji-tar ‘mutuwar’ Aminu Ala

July 28, 2025
KADIFF 2025: Uganda ta fi yawan finafinai a bikin baje-kolin na Kaduna – Israel Kashim Audu
Labarai

KADIFF 2025: Uganda ta fi yawan finafinai a bikin baje-kolin na Kaduna – Israel Kashim Audu

July 25, 2025
Karya dokar liƙi: Kotu ta ɗaure G-Fresh da Hamisu Breaker tsawon wata biyar-biyar
Labarai

Karya dokar liƙi: Kotu ta ɗaure G-Fresh da Hamisu Breaker tsawon wata biyar-biyar

July 24, 2025
‘Yan Kannywood sun kaɗu da rasuwar Abdoulfatah Omar
Labarai

‘Yan Kannywood sun kaɗu da rasuwar Abdoulfatah Omar

July 23, 2025
Allah ya yi wa mahaifiyar darakta Salisu Mu’azu rasuwa
Labarai

Allah ya yi wa mahaifiyar darakta Salisu Mu’azu rasuwa

July 17, 2025
Next Post
‘Sirrin Ɓoye’: Hatsabibiyar yarinya a Kannywood

'Sirrin Ɓoye': Hatsabibiyar yarinya a Kannywood

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!