• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Wednesday, July 30, 2025
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Galadiman Kano, Abbas Sanusi ya rasu yana da shekaru 92

by ALI KANO
April 2, 2025
in Nijeriya
0
Galadiman Kano, Abbas Sanusi ya rasu yana da shekaru 92

Mariganyi Galadiman Kano, Alhaji Abbas Sanusi

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

A daren jiya ne Allah ya yi wa Galadiman Kano, Alhaji Abbas Sanusi, rasuwa. Shekarun sa 92.

Za a yi jana’izar sa a yau a Birnin Kano.

An haifi Alhaji Abbas ne a Bichi a cikin 1933. Ya yi makarantar elementare ta Ƙofar Kudu a Kano a cikin 1944. Da ya gama, ya tafi Kwalejin Rumfa a cikin 1948. Ajin su ɗaya da mariganyi Galadiman Kano da ya gabace shi, wato Alhaji Tijjani Hashim, kuma a shekara ɗaya aka haife su.

Memba ne a majalisar Sarkin Kano tun a shekarun 1950.

Sarkin Kano na yanzu, Malam Muhammadu Sanusi II, shi ne ya naɗa shi Galadiman Kano. A lokacin, Sarki Bai, Hakimin Ɗambatta, Alhaji Mukhtar Adnan, kaɗai ne ya girme shi a majalisar Sarki.

Rabon da a naɗa Galadima tun 1992 lokacin da Sarkin Kano Ado Bayero ya naɗa Alhaji Tijjani Hashim wannan sarautar. Da Tijjani Hashim ya rasu yana da shekaru 81 aka naɗa Abbas.

Tun a zamanin mulkin Haɓe ne aka samar da sarautar Galadiman Kano, wato kafin Jihadin Fulani da aka yi a 1804, kuma shi ne muƙamin sarauta mafi girma bayan Sarki, har zuwa 1890 lokacin da aka aro sarautar Waziri daga Sakkwato. Daga nan Galadima ya zama na biyu a jerin manyan masu sarauta a Kano.

Abbas Sanusi kawu ne ga Sarkin Kano Muhammadu Sanusi II domin kuwa ɗa ne ga kakan Sarkin, wato Sarkin Kano Sir Muhammadu Sanusi I.

Mahaifin sa ne ya fara ba shi sarauta, da ya naɗa shi Sarkin Dawakin Tsakar Gida kuma Hakimin Ungogo a cikin 1959. Sarkin Kano na gaba, wato Muhammadu Inuwa, ya ɗaga darajar sa da ya naɗa shi Ɗan’iyan Kano a cikin 1962. Da ya rasu, Ado Bayero ya naɗa shi Wamban Kano, muƙamin da ya riƙe har zuwa lokacin naɗin sa matsayin Galadima.

Lokacin da Ado Bayero ya tafi asibiti a yayin ciwon ajalin sa, shi ne ya riƙe masarautar. Kuma da Ado ya rasu, yana daga cikin waɗanda suka yi takarar sarautar, amma sai Allah bai ba shi ba.

Allah ya rahamshe su baki ɗaya.

Loading

Tags: Galadiman Abbas Sanusi
Previous Post

Hotuna: Sarkin Kano ya kai ziyara ga Mai Babban Ɗaki

Next Post

Tinubu ya musanya shugaban NNPC Mele Kyari da Bayo Ojulari, kuma ya canza daraktocin hukumar gudanarwar kamfanin 

Related Posts

Nijeriya

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar da Sababbin Cibiyoyin Maganin Ciwon Daji

July 24, 2025
Sanatan Kaduna: Yerima Shettima za mu yi, inji ‘yan fim
Nijeriya

Sanatan Kaduna: Yerima Shettima za mu yi, inji ‘yan fim

July 15, 2025
Nijeriya

Tinubu yana goyon bayan Ƙananan Hukumomi su ci gashin kan su – Minista

July 11, 2025
Nijeriya

Shirin Sabunta Fata na Tinubu yana samar da damarmakin cigaba — Minista

July 10, 2025
Sauye-sauyen Tinubu suna taimaka wa farfaɗowar tattalin arzikin Nijeriya — Minista
Nijeriya

Sauye-sauyen Tinubu suna taimaka wa farfaɗowar tattalin arzikin Nijeriya — Minista

July 10, 2025
Ministoci za su fara gabatar da rahoton ayyuka a taron manema labarai
Nijeriya

Tinubu ba zai yarda hayaniyar siyasar 2027 ta ɗauke masa hankali ba – Minista

July 8, 2025
Next Post
Tinubu ya musanya shugaban NNPC Mele Kyari da Bayo Ojulari, kuma ya canza daraktocin hukumar gudanarwar kamfanin 

Tinubu ya musanya shugaban NNPC Mele Kyari da Bayo Ojulari, kuma ya canza daraktocin hukumar gudanarwar kamfanin 

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!