• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Wednesday, August 26, 2026
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Gwamnan Ondo ya yabi shirye-shiryen rage raɗaɗin rayuwa

by DAGA WAKILIN MU
November 27, 2020
in Nijeriya
0
Sadiya Umar Farouq da Rotimi Akeredolu

Sadiya Umar Farouq da Rotimi Akeredolu

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram
Gwamnan Jihar Ondo, Oluwarotimi Odunayo Akeredolu, ya yaba wa Gwamnatin Tarayya kan shirye-shirye daban-daban da ta fito da su don rage wa al’ummar Nijeriya matsalolin rayuwa.
 
Ya bayyana haka ne a wajen bikin ƙaddamar da shirin musamman na bada tallafin kuɗi ga matan karkara (Special Cash Grant Programme for Rural Women) a Jihar Ondo wanda Gwamnatin Tarayya ke aiwatarwa.
 
Ministar Harkokin Jinƙai, Agaji da Inganta Rayuwa, Hajiya Sadiya Umar Farouq, ita ce ta ƙaddamar da shirin inda aka agaza wa mata 200 da aka zaɓo daga yankunan ƙananan hukumomi 13 na jihar.
 
A lokacin da ta ke gabatar da jawabi ga matan a Jihar Ondo, ministar ta yi kira a gare su da su yi amfani da wannan dama da su ka samu wajen inganta hanyar samun kuɗin shiga da hanyoyin samun abincin su, kuma su bada gudunmawar su wajen inganta rayuwar su ta yau da kullum.
 
Ta ce, “Na yi amanna da cewar tare da goyon bayan mai girma Gwamna, waɗanda za su ci moriyar wannan shiri su na kan hanyar su ta ficewa daga tarkon fatara zuwa ga samun albarka kuma za mu iya ceton ‘yan Nijeriya miliyan 100 daga ƙangin fatara da yunwa daga yanzu zuwa shekara ta 2030 kamar yadda Shugaba Muhammadu Buhari ya hango.”
 
Sadiya Umar Farouq ta kuma bayyana cewa an tsara za a fara biyan kuɗin tallafin kuɗi kai-tsaye a ƙarƙashin shirin nan na ‘Conditional Cash Transfer’ a jihar na watan Satumba zuwa Disamba, 2019 kwanan nan, wanda daga nan za a dakatar da shirin saboda wasu matsaloli da aka samu da tsarin biyan kuɗin, wato ‘Payment Service Provider’ (PSP) da hukumar ICPC. 
 
Ta ce, “Ana nan ana warware wannan matsalar kuma ina  tabbatar wa da masu cin moriyar shirin cewa za su ci gaba da amfana da shi gadan-gadan.” 
 
A nasa jawabin, Gwamna Akeredolu ya gode wa Gwamnatin Tarayya saboda shirye-shirye daban-daban da ta fito da su don magance matsalolin rayuwa waɗanda Jihar Ondo ta ke amfana da su, wato irin su ‘Conditional Cash Transfer’, ‘Home Grown School Feeding’, ‘Special Grant Transfer’, da ‘Public Workfare and Skills for Jobs’ a ƙarƙashin shirin tallafa wa matasa. 
 
Gwamnan ya ce shirin bada tallafin kuɗi ga matan karkara wata dama ce ta ƙarfafa wa mata rayuwa, rage fatara da kuma farfaɗo da tattalin arziki bayan da annobar korona ta shafi rayuwar ɗimbin jama’a.
 
Ya ce, “Al’ummar Jihar Ondo su na miƙa godiyar su ga Gwamnatin Tarayya saboda waɗannan shirye-shirye na inganta rayuwa da su ka sauya rayuwar matan karkara a jihar mu. Da yawa daga cikin waɗannan matan sun tashi daga matsayin masu rayuwar fatara zuwa masu ɗan jin daɗin rayuwa. Su na gudanar da sana’o’in su yanzu a cikin babbar damar faɗaɗa su.
 
“Gwamnatin Jihar Ondo ta na matuƙar jin daɗin wannan shiri na inganta rayuwar matan karkara a matsayin wata hanya ta rage fatara da yunwa. Wannan shiri ya yi daidai da muradin gwamnatin Jihar Ondo na fitar da yawancin mata daga tarkon fatara. Don haka ne ma gwamnatin a ko yaushe ta ke aiki da shirye-shiryen inganta rayuwa don tabbatar da samar da nagartattun hanyoyin samun sana’a ga talakawa, musamman ma dai mata.”
 
Gwamna Akeredolu ya kuma yi alƙawarin yin aiki kafaɗa da kafaɗa da hukumomin Gwamnatin Tarayya don tabbatar da cewa an samu inganci a rayuwar jama’ar Jihar Ondo, musamnan matan karkara.

Loading

Previous Post

KILAF 2020: An yi taron duniya kan finafinan Afrika ba tare da ‘yan Kannywood ba

Next Post

Hotuna: Liyafar cin abincin bikin Mustapha Musty da Ghadir

Related Posts

Yadda CBN ke tallabe da tattalin arzikin Nijeriya, yayin sa farashin ɗanyen mai ke faɗuwar-‘yan-bori a kasuwa
Nijeriya

Yadda CBN ke tallabe da tattalin arzikin Nijeriya, yayin sa farashin ɗanyen mai ke faɗuwar-‘yan-bori a kasuwa

November 7, 2025
Shirin ƙarfafa jari: CBN ya shawarci bankuna marasa ƙarfi su haɗe ko su rage wa lasisin su geji
Nijeriya

Shirin ƙarfafa jari: CBN ya shawarci bankuna marasa ƙarfi su haɗe ko su rage wa lasisin su geji

November 2, 2025
Bankin CBN ya yunƙuro: Naira ta hana dala numfashi mai ƙarfi a ƙarshen Oktoba
Nijeriya

Bankin CBN ya yunƙuro: Naira ta hana dala numfashi mai ƙarfi a ƙarshen Oktoba

November 2, 2025
Bankin CBN ya ƙaryata ƙazafin sayar wa manyan dillalan mai dala biliyan 1.259 domin su shigo da fetur daga waje
Nijeriya

Bankin CBN ya ƙaryata ƙazafin sayar wa manyan dillalan mai dala biliyan 1.259 domin su shigo da fetur daga waje

October 29, 2025
Tinubu ya yi adalci ga dukkan yankunan Nijeriya – Ministan Yaɗa Labarai
Nijeriya

Tinubu ya yi adalci ga dukkan yankunan Nijeriya – Ministan Yaɗa Labarai

August 31, 2025
Nijeriya

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar da Sababbin Cibiyoyin Maganin Ciwon Daji

July 24, 2025
Next Post
Hotuna: Liyafar cin abincin bikin Mustapha Musty da Ghadir

Hotuna: Liyafar cin abincin bikin Mustapha Musty da Ghadir

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!