• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Sunday, June 15, 2025
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

KILAF 2020: An yi taron duniya kan finafinan Afrika ba tare da ‘yan Kannywood ba

by DAGA MUHAMMAD LAWAN RANO
November 25, 2020
in Labarai
0
Alhaji Abdulkareem Muhammad na gabatar da jawabin sa ga taron

Alhaji Abdulkareem Muhammad na gabatar da jawabin sa ga taron

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram
AN kwashe tsawon kwana biyu ana gudanar da taron duniya kan finafinan harsunan Afrika na gado, amma masu shirya finanan Hausa ba su halarta ba.

 

A yau ne aka kammala taron a Kano.

A taron, Shugaban Tsangayar Aikin Jarida ta Jami’ar Bayero, Kano, Farfesa Mustapha Nasiru Malam, ya bayyana cewa nan ba da jimawa ba za a samar da ƙananan kwasa-kwasai a jami’ar domin ƙara wa masu sana’ar shirya fim ilimi.

 
Malamin ya bayyana haka ne a jawabin da ya gabatar bayan  kammala taron yini biyu kan yadda ake gudanar da bincike da rubuta labaran finafinai cikin harsunan Afrika, wanda aka yi a yau a Kano.
 
Taron, wanda aka fi sani da ‘Kano Indigenous Languages of Africa Film Market and Festival’ (KILAF), an gudanar da shi ne ta hanyar tsarin ga-ni-ga-ka ta manhajar Zoom.
 
Ɗimbin jama’a sun mahalarci taron ta hanyar Zoom
Kuma an yi shi ne tare da haɗin gwiwa tsakanin kamfanin shirya finafinai na Moving Image da ke Kano da Tsangayar Aikin Jarida ta Jami’ar Bayero, Kano (BUK).
Farfesan ya ƙara da cewa haɗin kan nasu ba zai tsaya iya shirya wannan taron ba, domin kuwa tsangayar za ta ci gaba da haɗa kai da kamfanin Moving Image, mai shirya taron na shekara-shekara, don ganin an ciyar da harkar shirya finafinai gaba. 
 
A nasa jawabin, shugaban Moving Image kuma jagoran shirya taron, Alhaji Abdulkareem Muhammad, ya bayyana farin cikin sa ganin yadda su ka gabatar da taron a karo na uku cikin kwanciyar hankali tare da samun haɗin kan al’umma, musamman waɗanda su ka halarta.
 
Bugu da ƙari, ya yaba wa Tsangayar  Aikin Jarida ta BUK kan irin gudunmawar da ta bayar wajen ganin an yi taron lafiya ba tare da tangarɗar kayan aiki ba.
 
Wasu mahalarta taron
A yayin taron, an gabatar da maƙaloli kimanin 22 waɗanda su ka fito daga sassa daban-daban na Nijeriya da ƙasar waje.
 
Masu gabatar da maƙalolin sun fito daga Kano, Legas, Abuja, Jamus da sauran su daga jami’o’i, kwalejojin fasaha da na iliimin aikin koyarwa.
 
Sai dai har zuwa lokacin kammala taron, mujallar Fim ba ta ga ‘yan masana’antar shirya finafinan Hausa ta Kannywood a ciki ba duk da irin kiraye-kirayen da aka yi kan su fito su rungumi wannan tsarin domin taimaka wa cigaban sana’ar tasu.
 
Lokacin gudanar da taron
Idan kun tuna, mujallar Fim ta kawo maku tattaunawar da ta yi da Alhaji Abdulkareem Muhammad a game da taron, inda ya bayyana irin ƙalubalen da su ke fuskanta kan shirya taron, musamman ƙin shiga taron da ‘yan Kannywood su ka yi.

Loading

Previous Post

Yadda Mamadou Tandja ya ɓata rawar sa da tsalle a shugabancin Nijar

Next Post

Gwamnan Ondo ya yabi shirye-shiryen rage raɗaɗin rayuwa

Related Posts

Wani maigida na ya ce wahalar banza nake yi a kan Yerima Shettima, inji Hussaini Danko
Labarai

Wani maigida na ya ce wahalar banza nake yi a kan Yerima Shettima, inji Hussaini Danko

June 13, 2025
Jarumin Kannywood, Abdul M. Shareef zai auri jaruma Maryam Malika
Labarai

Jarumin Kannywood, Abdul M. Shareef zai auri jaruma Maryam Malika

June 12, 2025
Hukumar Tace Finafinai ta Kano ta yaba wa ɗakunan taruka bisa bin doka da oda lokacin bukukuwan Sallah
Labarai

Hukumar Tace Finafinai ta Kano ta yaba wa ɗakunan taruka bisa bin doka da oda lokacin bukukuwan Sallah

June 12, 2025
Rahama Sadau ta raba barka da Sallah ga ‘yan fim na Kaduna
Labarai

Rahama Sadau ta raba barka da Sallah ga ‘yan fim na Kaduna

June 11, 2025
‘Aure tsakanin jaruman Kannywood, Mansurah da Momoh’: Yadda lamarin yake
Labarai

‘Aure tsakanin jaruman Kannywood, Mansurah da Momoh’: Yadda lamarin yake

June 11, 2025
An naɗa Shehu Hassan Kano shugaban riƙo na MOPPAN
Labarai

An naɗa Shehu Hassan Kano shugaban riƙo na MOPPAN

June 3, 2025
Next Post
Sadiya Umar Farouq da Rotimi Akeredolu

Gwamnan Ondo ya yabi shirye-shiryen rage raɗaɗin rayuwa

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!