• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Wednesday, August 26, 2026
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Gwamnan Zamfara ya jajanta wa al’ummar yankunan Zurmi, Maru, Tsafe da kewaye

* Ya jinjina wa jami'an tsaro

by DAGA WAKILI
December 14, 2023
in Nijeriya
0
Gwamnan Zamfara ya jajanta wa al’ummar yankunan Zurmi, Maru, Tsafe da kewaye
0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

SAKAMAKON hare-haren ‘yan bindiga da aka yi fama da su a baya-bayan nan, Gwamnan Jihar Zamfara, Dakta Dauda Lawal Dare, ya jajanta wa al’ummar da ‘yan bindiga su ka hana zaman lafiya a yankin Zurmi da kewaye.

Gwamnan ya kuma jinjina wa dakarun tsaro saboda ƙoƙarin da su ke yi na kakkaɓe ‘yan bindigar, masu garkuwa da kuma aikata ta’addanci.

Cikin wata sanarwa da Kakakin Yaɗa Labarai na Gwamnan, Malam Sulaiman Bala Idris, ya fitar tare da sa mata hannu, Gwamna Lawal ya bayyana tsananin damuwar sa dangane da hare-haren baya-bayan nan da ‘yan bindiga suka riƙa kaiwa cikin Ƙaramar Hukumar Zurmi.

Ya ce duk da wannan aika-aika da maharan ke yi, rahotanni na nuni da cewa an kakkaɓe manyan kwamandoji da gogarma-gogarman ‘yan bindiga da dama a Zamfara da sauran yankunan Arewa-maso-yamma.

Ya ce: “Gwamnatin Zamfara ta nuna damuwa sosai dangane da hare-haren da ‘yan bindiga su ka kai kwanan nan a yankunan Zurmi, Maru, Tsafe da sauran yankunan jihar.

“Mu na miƙa jaje da ta’aziyya, alhini da damuwa ga dukkan waɗanda wannan farmaki ya shafa, musamman a Ƙaramar Hukumar Zurmi, inda aka rasa rayuka.

“Gwamnatin Jihar Zamfara za ta bayar da tallafin gaggawa da kayan agaji ga waɗanda waɗannan hare-hare su ka shafa. Kuma mu na tabbatar da cewa gwamnati ta maida hankali sosai wajen tabbatar da tsare duniyoyi da rayukan jama’a.

“Mu na kuma sane da irin sadaukarwar da jami’an tsaro ke yi wajen kare rayukan jama’a. Gwamnatin jiha za ta ƙara taimaka masu da dukkan abubuwan da su ke buƙata wajen yaƙi da ‘yan bindiga.”

Loading

Tags: 'yan bindigaDauda Lawal Darehare-harerashin tsarota'addanciZamfara
Previous Post

Kasafin kuɗin Ma’aikatar Yaɗa Labarai na 2024 ya yi kaɗan, a ƙara shi, inji Majalisar Dattawa

Next Post

Minista Hannatu Musawa ta ƙudiri aniyar kafa Gidan Tarihi da Gidan Wasanni na Ƙasa a Abuja

Related Posts

Yadda CBN ke tallabe da tattalin arzikin Nijeriya, yayin sa farashin ɗanyen mai ke faɗuwar-‘yan-bori a kasuwa
Nijeriya

Yadda CBN ke tallabe da tattalin arzikin Nijeriya, yayin sa farashin ɗanyen mai ke faɗuwar-‘yan-bori a kasuwa

November 7, 2025
Shirin ƙarfafa jari: CBN ya shawarci bankuna marasa ƙarfi su haɗe ko su rage wa lasisin su geji
Nijeriya

Shirin ƙarfafa jari: CBN ya shawarci bankuna marasa ƙarfi su haɗe ko su rage wa lasisin su geji

November 2, 2025
Bankin CBN ya yunƙuro: Naira ta hana dala numfashi mai ƙarfi a ƙarshen Oktoba
Nijeriya

Bankin CBN ya yunƙuro: Naira ta hana dala numfashi mai ƙarfi a ƙarshen Oktoba

November 2, 2025
Bankin CBN ya ƙaryata ƙazafin sayar wa manyan dillalan mai dala biliyan 1.259 domin su shigo da fetur daga waje
Nijeriya

Bankin CBN ya ƙaryata ƙazafin sayar wa manyan dillalan mai dala biliyan 1.259 domin su shigo da fetur daga waje

October 29, 2025
Tinubu ya yi adalci ga dukkan yankunan Nijeriya – Ministan Yaɗa Labarai
Nijeriya

Tinubu ya yi adalci ga dukkan yankunan Nijeriya – Ministan Yaɗa Labarai

August 31, 2025
Nijeriya

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar da Sababbin Cibiyoyin Maganin Ciwon Daji

July 24, 2025
Next Post
Minista Hannatu Musawa ta ƙudiri aniyar kafa Gidan Tarihi da Gidan Wasanni na Ƙasa a Abuja

Minista Hannatu Musawa ta ƙudiri aniyar kafa Gidan Tarihi da Gidan Wasanni na Ƙasa a Abuja

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!